Daga Hassan Umar Gwammaja
Sanusi, wanda ya yi wannan furuci a wani taro da aka shirya domin tattaunawa kan shugabanci da adalci a cikin al’umma, ya ce:
> “A yau idan ka duba yadda ‘yan siyasa ke gudanar da harkokinsu, za ka fahimci cewa mafi yawan su ba su da tarbiyya, ba su da mutunci, kuma ba sa jin tsoron Allah. Wannan na daga cikin dalilan da ya jefa Najeriya cikin halin da take ciki.”
Ya kuma ja hankalin matasa da su rika yin hankali wajen zaben shugabanni, su guji siyar da kuri’unsu ga ‘yan siyasar da ke da rauni a tarbiyya da sanin ya kamata.
Sarkin ya jaddada cewa al’umma ba za su ci gaba ba sai idan suka zabi shugabanni masu gaskiya, rikon amana da tsoron Allah.












