Daga A S Gwammaja
Alƙalan Kotun Ƙolin Najeriya a Juma’ar nan suna da babban aiki a gabansu, kasancewar hukunce-hukunce da dama da za su yanke, na shari’o’in zaɓukan gwamna da aka ɗaukaka daga faɗin ƙasar.
Wata majiyar Kotun Ƙoli ta tabbatarwa da BBC cewa shari’o’in zaɓe bakwai, ake sa ran alƙalan za su yanke hukuncinsu.
Hukunce-hukuncen na da matuƙar muhimmanci ga jihohin da abin ya shafa da kuma siyasar Najeriya.
Matakin kuma shi ne na ƙarshe ga fafutukar mulki ta hanyar shari’a. tsakanin ‘yan siyasa da jam’iyyunsu, tun Bayan kammala zaɓukan 2023.
Hukunce-hukuncen shari’o’in zaɓen gwamna da ƙananan kotuna suka yanke a baya, ba su iya kawo ƙarshen ja-in-jar da ake ta bugawa ba.
Sai dai yanzu, an zo magaryar tiƙewa. Kotun da ake kira ‘Daga Ke Sai Allah Ya Isa’, za ta yi fashin baƙin dokoki, sannan ta zartar hukunci.
Ga jerin shari’o’in da kotun za ta yanke hukuncinsu ranar Juma’a:
Abba Gida – Gida da Nasiru Yusuf Gawuna a jihar kano
A wannan ƙara, Kotun Ƙolin ana hasashen cikin biyu, za ta yi ɗaya, ko dai ta tabbatar da hukunce-hukuncen kotuna baya, ta jaddada nasarar da suka bai wa Nasiru Gawuna, ko kuma ta rushe matsayarsu, ta bai wa Abba Kabir Yusuf gaskiya.
Sai Shari’ar Caleb Mutfwang da Nentawe Goshwe daga jihar Filato, itama na ɗaya daga cikin shari’o’i masu zafi, da ake sa ran kotun ƙolin a Juma’ar nan, za ta yanke hukunci a kai.
Sai ta jihar Zamfara Bello Matawalle, Gwamna Dauda Lawal Dare da ya ɗaukaka ƙara zuwa kotun ƙoli yana neman ta tabbatar da nasararsa, wadda kotun baya ta soke, har ma ta ba da umarnin a yi sabon zaɓe cikin wasu ƙananan hukumomi.












