• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kwamishinan Harkokin Sufuri na Kano Ya Ajiye Aiki Saboda Cece-kucen Zargin karbar Belin Wanda Ake Zargi da Dillancin Miyagun Kwayoyi

aksam by aksam
August 6, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

 

Daga Hassan Umar Gwammaja

Kwamishinan Harkokin Sufuri na Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali Namadi, ya ajiye mukaminsa da yammacin Laraba, bayan Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi rahoton kwamitin bincike da aka kafa don gano rawar da ya taka a belin wani da ake zargi da safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Danwawu.

‎‎Wannan sau yi ana kallonsa a matsayin wani babban mataki wajen ƙarfafa ɗabi’un gaskiya, da rikon amana a wannan gwamnati.

‎‎A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, Kwamishina Namadi ya bayyana cewa murabus ɗinsa na da nasaba da bukatar kare muradun al’umma da kuma la’akari da mahimmancin batun.‎‎

Ya ce: “A matsayina na ɗan gwamnati da ke gaba da gaba wajen yaƙi da sha da fataucin miyagun kwayoyi, dole ne in ɗauki wannan mataki — kodayake yana da ɗaci. Duk da cewar ina da yakinin ba ni da laifi, ba zan iya watsi da tasirin yadda jama’a ke kallon lamarin ba, da kuma buƙatar kare ƙimar da muka gina tare.

”‎‎‎‎Alhaji Namadi ya bayyana godiyarsa ga Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa damar da ya ba shi na yin hidima wa jiharsa, tare da sake jaddada jajircewarsa wajen gudanar da shugabanci na gari da rikon amana.‎‎

Ya ƙara da cewa:“A matsayina na nagartaccen ɗan ƙasa, dole ne in tsaya tsayin daka wajen kare amana da hangen nesa da muka gina a jihar nan. Zan ci gaba da kasancewa cikin masu biyayya ga akidar da ta kawo wannan gwamnati kan mulki.

”‎‎‎‎A nasa bangaran Gwamna Abba Kabir Yusuf ya karɓi murabus ɗin cikin girmamawa, tare da yi masa fatan alheri a rayuwarsa ta gaba. Ya kuma jaddada cewa gwamnatinsa ba za ta sassauta ba wajen yaƙi da laifukan da suka shafi kwayoyi da sauran ɗabi’un banza da ke lalata rayuwar matasa da al’umma gaba ɗaya.‎‎

Gwamnan ya kuma shawarci dukkan masu rike da mukaman siyasa da su rika taka-tsantsan a kan duk wani lamari da ya shafi jama’a, tare da neman izini daga hukumomin da suka dace kafin su tsoma kansu cikin irin waɗannan batutuwa.‎‎

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

An Yi Mummunar Faɗuwa a Sakamakon Jarrabawar Bana – WAEC

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Gargadi Jami’anta Dasu Guji Tsoma Baki Kan Abinda Bai Shafe Su Ba A Wani Yunkuri Na Tallafawa Gwamnati Sauke Hakkokin Al’umma

aksam

aksam

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa
Uncategorized

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

by aksam
June 15, 2026
Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato
Uncategorized

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

by aksam
June 2, 2026
Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa
Uncategorized

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

by aksam
May 31, 2026
Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya
Uncategorized

Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya

by aksam
May 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Majalisar Dokokin Kano Ta Gayyaci Shugaban SUBEB Kan Zargin Rashin Gamsuwa a Daukar Ma’aikata

Majalisar Dokokin Kano Ya Sanya Ranar Tantance Murtala Garo A Matsayin Mataimakin Gwamna

April 22, 2026
KANO STATE POLICE COMMAND FOILS EXPLOSIVE AND DRUG TRAFFICKING ATTEMPTS, ARRESTS SUSPECT

KANO STATE POLICE COMMAND FOILS EXPLOSIVE AND DRUG TRAFFICKING ATTEMPTS, ARRESTS SUSPECT

January 16, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media