Daga: Hassan Umar Gwammaja
Darantar Yada Labaru Na Gwamnan Kano Sunusi Bature ya bayyana haka a madadin gwamna Abba Kabir Yusuf a lokacin da ya ke taro da manema labaru a gidan gwamnati .
Sunusi Bature ya ce gwamnatin kano tuni ta dade da shiri wajen cigaba da yaki da masu tu’amuli da miyagun kwayoyi, fadan daba , kwacen waya da sauran laifuka da za su illata al’umma a fadin jihar.
Daraktan ya ce gwamanti ta yabawa ‘yan kwamitin bincike da suka gudanar da aikinsu cikin mako guda karkashin jagorancin mai bawa gwamna shawara kan harkokin Barista Aminu Hussaini.










