• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Jami’an tsaro ne ke jawo jama’a cikin aikata miyagun Laifuka: Gwamnan Borno, kalli dalilinsa

aksam by aksam
May 7, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum, ya haramta sayar da barasa, yayin da ya zargi sojoji da sauran jami’an tsaro da aikata miyagun laifuka da cin zarafin jama’a a birnin Maiduguri da kewaye.

Gwamnan ya ce tsofaffin jami’an tsaron Nijeriya da na yanzu da suke aiki sun taka rawa wajen jawo jama’a cikin aikata miyagun laifuka kamar tsaurin ra’ayi da karuwanci da sauran munanan ɗabi’u, lamarin da ke kara ta’azzara barazanar ta’addanci a jihar.

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Talata a wajen kaddamar da wani kwamitin da aka kafa don “ƙwace haramtattun otal-otal da gidajen karuwai da gidajen kwana da maɓoyar miyagun laifuka da kuma daƙile illolin munanan dabi’u.

“Na yi farin ciki da sanin cewa jami’an soji suna wajen nan, musamman sojoji, ‘yan sanda, da sauran su, domin yawancin wadannan ayyukan wa ke yin su? Wasu daga cikinsu akwai jami’an soji da aka kora da masu ci a yanzu har da fararen hula.

“Don haka, bai kamata a ƙi sukar kowane ɓangare ba a cikin wannan lamarin idan har muna son babban birnin Maiduguri da kuma jihar ta kawar da ta’addanci da sauran laifuka,” in ji Zulum.

A takaitaccen taron, Zulum ya sake kafa kwamitin tare da sake ba wa kwamitin damar kawar da duk wani nau’i na miyagun laifuka da munanan dabi’u a cikin babban birnin Maiduguri da kewaye.

Dokar hana sayar da barasa da kayan maye, a cewar gwamnan, ta samo asali ne daga yadda ake ta samun tashe-tashen hankula a tsakanin kungiyoyin da ke gaba da juna da kungiyoyin asiri da karuwanci da shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da ‘yan fashi da sata, wadanda suka haddasa asarar rayuka da dukiya.

Gwamnan ya hada hannu da sojoji, ‘yan sanda, Civil Defence, da wasu jami’an tsaro da dama da suka hada da civilian JTF domin shiga cikin kwamitin domin gudanar da cikakken bincike.

Da yake amincewa da aikin da ke gaban kwamitin da aka sake kafawa, shugaban kwamitin ya yi tir da tabarbarewar harkokin tsaron cikin gida a Maiduguri tare da bayyana matakin da kwamitin zai dauka nan take.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnatin Katsina taagantu kan korafi da cecekucen da ya mamaye kafafen sada zumunta

Next Post

Gwamnatin tarayya ta fadi dalilin da ya hana ɗalibai cin jarabawar JAMB

aksam

aksam

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa
Uncategorized

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

by aksam
June 15, 2026
Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato
Uncategorized

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

by aksam
June 2, 2026
Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa
Uncategorized

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

by aksam
May 31, 2026
Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya
Uncategorized

Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya

by aksam
May 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Rashin biyan Albashi jam’iyar PDP ta caccaki shugaba Tinubu

Rashin biyan Albashi jam’iyar PDP ta caccaki shugaba Tinubu

December 31, 2023
Mafi karancin albashi wani Gwamna ya yi Amai ya lashe

Mafi karancin albashi wani Gwamna ya yi Amai ya lashe

October 13, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media