Ana zargin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da mayar da ƙasar nan wani ƙaton sansanin ƴan gudun hijira (IDP)
Jam’iyyar PDP ta ce gazawar da gwamnatin Tinubu ta yi wajen biyan ma’aikata albashin watan Disamba ya tabbatar da shirinsa na takaici da cutar da ƴan Najeriya
Sakataren yaɗa labaran PDP na ƙasa, Debo Ologunagba ya ce ya kamata gwamnatin APC ta biya ma’aikata albashin watan Disamba sannan ta biya su diyya da aƙalla kaso 50%
Ologunagba ya ce gazawar da gwamnatin Tinubu ta yi na biyan albashin watan Disamba ya tabbatar da cewa jam’iyyar APC ta shirya tsaf domin fusata ƴan Najeriya da ƙara musu raɗaɗi.
Ya ce rashin biyan albashi wata hanya ce da gwamnatin APC ta ke amfani da ita wajen ɗaukar nauyin talauci da murƙushe jama’a don miƙa wuya ga mulkin kama-karya.
Wani ɓangare na sanarwar na cewa: “Irin wannan rashin zuciya da gwamnatin APC marar kishin jama’a ta nuna bai taɓa faruwa ba a cikin shekaru 16 da PDP ta yi tana mulki.
A cewar sa a gwamnatin su ta PDP ma’aikata na karɓar albashin watan Disamba kafin ranar Kirsimeti (25) don ba su damar yin bukukuwan ƙarshen shekara tare da masoyan su.”












