• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kotun ɗaukaka ƙara ta umarci a kai mata Sheikh Abduljabbar gabanta

aksam by aksam
April 21, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home KOTU
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar (ADC) Na Kasa

Kotun Koli ta yanke hukuncin kan rikicin jam’iyyar PDP

Daga Hassan Umar Gwammaja

Sheikh Abduljabbar, malamin addinin Musulunci, na tsare a gidan yari ne bayan wani hukunci da Ƙaramar Kotun Shari’a ta yanke, inda ta same shi da laifin batanci tare da yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya.

A yayin zaman kotun a ranar Litinin, jagoran alkalai, mai shari’a Mohammed Lawal-Shuaibu, ya bayyana cewa tun da wanda ya shigar da ƙarar ya yi hakan da kansa ba tare da lauya ba, dole ne ya bayyana a gaban kotu domin kare kansa da hujjojinsa.

Sauran alkalan da suka zauna tare da shi sun haɗa da Mai shari’a Abubakar Mu’azu-Lamido da Mai shari’a Ahmad Ramat-Mohammed.

Alkalin ya ce, “Tunda mai ƙara ya shigar da ƙarar da kansa ba tare da wakilcin lauya ba, wajibi ne ya bayyana a gaban kotu da kansa. Haka kuma, kasancewar yana tsare, an umarci hukumar gidan yari da ta gabatar da shi a ranar 23 ga Afrilu, 2026 domin ci gaba da sauraron ƙarar.”

Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 23 ga Afrilu domin ci gaba da sauraron ƙarar.

 

Tun da farko, lokacin da aka kira shari’ar, babu ɓangarorin da suka halarta ko wakilansu a kotu.

A wannan lokaci ne wani mutum mai suna Usman Malam-Hussaini ya tashi ya sanar da kotu cewa Sheikh Abduljabbar ya aiko shi da wasiƙa domin neman a mayar da shi Kano daga gidan yarin Kuje, don samun damar duba takardunsa cikin sauƙi.

Sai dai alkalin ya gayyaci Babban Lauyan Jihar Kano kuma Kwamishinan Shari’a, Abdulkarim Kabiru-Maude (SAN), da ya bayyana a gaban kotu, tare da ɗage sauraron shari’ar na ɗan lokaci.

Daga bisani, lokacin da aka sake kiran shari’ar, Mataimakin Daraktan Gurfanar da Ƙara na Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kano, Barista Zahradeen Kofar-Mata, ya shaida wa kotu cewa Babban Lauyan jihar ba ya cikin koshin lafiya, kuma ya nemi a miƙa uzurinsa ga kotu saboda rashin halarta.

Ya ƙara da cewa an bai wa wani lauya mai zaman kansa shari’ar, sannan ya danganta jinkirin da aka samu da wata tangarda a sashen rajista.

Sai dai alkalin ya nuna rashin jin daɗinsa kan rashin halartar Babban Lauyan jihar, yana mai cewa hakan rashin girmama kotu ne, kafin daga bisani ya ɗage shari’ar zuwa ranar da aka tsara.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Jam’iyyar APC Ta Sanar Da Kudin Sayen Fom Din Tsayawa Takara A Zaben 2027

Next Post

Gwamnati Ta Fara Shari’ar Wadanda Ake Zargin Da Shirin Kifar Daulki A Najeriya

aksam

aksam

RelatedPosts

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta
KOTU

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

by Khadija Maitaya
August 7, 2026
Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar  (ADC) Na Kasa
KOTU

Yanzu-Yanzu: Kotun Koli Ta Tabbatar Da Sanata David Mark a Matsayin Halastaccen Shugaban Jam’iyyar (ADC) Na Kasa

by aksam
April 30, 2026
Yau Ake Sa Ran Kotun Koli Ta Najeriya Zata Yanke Hukunci A Yau Kan Rikicin Shugabancin  Jam’iyyar ADC A Matakin Kasa
KOTU

Kotun Koli ta yanke hukuncin kan rikicin jam’iyyar PDP

by aksam
April 30, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Umar Idris Farawa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Bisa Samun sa Da Laifi
KOTU

Kotu Ta Yanke Wa Umar Idris Farawa Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Bisa Samun sa Da Laifi

by aksam
April 22, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Wata Babbar Kotun Kasar Ghana Ta Yi  Wa Wasu Mutum 12 Daurin  Rai-Da-Rai  Kan Kisan Wani Soja

Wata Babbar Kotun Kasar Ghana Ta Yi Wa Wasu Mutum 12 Daurin Rai-Da-Rai Kan Kisan Wani Soja

January 31, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media