• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Tarin dukiya, wata mata ta zama ta 12 a jerin wadanda suka fi kowa kudi a Duniya

aksam by aksam
December 30, 2023
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Matar da ta gaji kamfanin L’Oréal, Françoise Bettencourt Meyers ta zama matar da ta fara tara dukiyar da ta kai dala biliyan 100 (a canjin naira sun zarce tirliyan ɗaya), kamar yadda jerin lissafin mutanen da suka fi kuɗi a duniya, ya nuna.

Bafaranshiyar mai katafaren kamfanin harkar kwalliya da kakanta ya kafa, tana kan matakin nasara ne saboda harkokin hannun jarin kamfaninta tsawon shekaru gommai, suna matuƙar garawa.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Hannayen jarin L’Oréal sun yi tashin da ba a taɓa gani ba a tarihi, ranar Alhamis.

Kasuwa ta sake buɗewa ga kayan kamfanin, bayan annobar korona, lokacin da mutane ke amfani da kayan kwalliya kaɗan, saboda zaman kulle.

Tsagwaron dukiyar Francoise Bettencourt Meyers, ‘yar shekara 70, ta zarce dala biliyan 100 a jerin lissafin biloniyoyi na jaridar Bloomberg, abin da ya sa ta zama, ta 12 mafi kuɗi a duniya.

Har yanzu akwai nisa tsakaninta da takwaranta Bafaranshe Bernard Arnault, wanda shi ne na biyu a jerin masu kuɗin duniya da tsabar dukiyar da ta kai dala biliyan 179b.

Mista Arnault shi ne mai LVMH, gungun kamfanonin kayan alatu mafi girma a duniya, wanda ya mallaki kamfanonin sarrafa rantsattsun kaya masu tsadar gaske irinsu Fendi da Louis Vuitton.

Miss Bettencourt Meyers ita ce mataimakiyar shugaba a hukumar gudanarwar kamfanin. Kuma ita da ‘ya’yanta ne a dunƙule suka mallaki hannun jari mafi girma a L’Oréal da kaso kimanin 35%.

Ta kasance mai tashen da ci gadon L’Oréal daga wajen mahaifiyarta, Liliane Bettencourt, wadda ta rasu a 2017.

Liliane, wadda aka riƙa bayyana ta a matsayin matar da ta fi kowa kuɗi a Faransa, tana da alaƙa ta ƙuƙut da shugabannin ƙasar, kuma ta riƙa ɗaukar hankalin kafofin yaɗa labarai

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Harin Plateau Jam’iyar PDP ta zargi sashin fikra na jamian tsaro

Next Post

Rashin biyan Albashi jam’iyar PDP ta caccaki shugaba Tinubu

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Comment Fonctionnent les Tournois sur raviolibet casino

April 22, 2025
‘Yan Ta’addan Da Suka Yi Garkuwa Da ‘Yan Kai Amarya A  Jihar Katsina Sun Yi Alkwarin Sake Aurar Da Amarya A Wani Faifan Bidiyo

‘Yan Ta’addan Da Suka Yi Garkuwa Da ‘Yan Kai Amarya A Jihar Katsina Sun Yi Alkwarin Sake Aurar Da Amarya A Wani Faifan Bidiyo

February 7, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media