• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Katsina taagantu kan korafi da cecekucen da ya mamaye kafafen sada zumunta

aksam by aksam
May 6, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
469
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda ya ce ba su ce wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu babu ƙorafi a Katsina ba kamar yadda ake ta muhawara a kai a ƙasar.

A wani saƙon murya ta gwamnan da aka fitar don yin martani a kan ce-ce-ku-cen da ya kaure a Nijeriya kan wani allon saƙo da aka kakkafa a Katsina lokacin da Shugaba Tinubu ya halarci auren ‘yar gwamnan, Gwamna Radda ya ce yana da kyau a dinga bincike kafin yanke hukunci kan abubuwa.

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

“Na saurari muryar da aka turo aka ce daga Alhaji Garba Dangida ne da kuma Janar Tsiga kuma na yi godiya sosai da wannan voice da na ji, kuma ina fatan Allah ya saka musu da alheri.

“Amma abin da nake so na ce shi ne ya kamata a dinga bincike idan an ji labari a soshiyal midiya ko a zahiri kuma a dinga tambaya,” in ji gwamnan.

Lamarin dai ya jawo zazzafar muhawara da ce-ce-ku-ce daga ko ina a fadin Nijeriya inda masu sharhi ke cewa jihar da ke fama da ƙalubalen tsaro bai kamata ta nuna wa Shugaban Ƙasa cewa ba ta da wani ƙorafi ba.

Sai dai Gwamna Radda ya ce sun tattauna matsaloli uku da ke damun jihar Katsina da Shugaban Ƙasar da suka haɗa da matsalar rashin tsaro da aikin windmill na Rimi da ayyukan filinjiragen sama da aka tsaida.

“Maganar hanyoyi kuwa da kansa (Shugaban Ƙasa) dama ya yi kuma hanyoyin an ba da aikinsu kuma mun shaida wa Shugaban Ƙasa wannan.

Amma a kan batun allon talla da aka rubuta Katsina babu ƙorafi gwamnan ya ce”Maganar billboard da wani ya buga na cewa ‘Katsina ba ƙorafi’ ni a matsayina na gwamna ban ma san an buga shi ba sai da na gani a soshiyal midiya nake tunanin yaya aka buga shi, wa ya buga shi.”

Radda ya koka cewa kuskure ne idan aka dinga jam’i ana zargin mutane a kan abin da a zahirance sun tabbatar ba su yi ba.

“Amma ku manyanmu ne iyayenmu ne idan kun ga wani abu na kuskure kuna iya mana magana muna iya gyarawa, mu kuma mutane ne muma kamar kowa muna iya yin kuskure muna iya yin ba daidai ba.

“Amma dai don Allah a matsayin manya da iyaye idan kun ji abu a soshiyal midiya ku dinga kiranmu ku ji yaya abin ya kasance ba wai a tafi soshiyal midiya a dinga irin wadannan maganganun ba. Ina ga ba za su taimake mu ko kawo mana cigaban da muke bukata ba a Katsina,” a cewar gwamnan.

A ƙarshen saƙon muryar na ranar Talata mai tsawon minti 2.48, Radda ya ce “shugabancin nan idan Allah ya ba ka shi kowa na iya kuskure yana iya daidai. Muna fatan Allah ya dora mu bisa daidan. Amma dai a wannan labarin da aka ba da ba haka yake ba.

Share188Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Tawagar ‘Yan Wasan Kwallon Kafar; Kasar Portugal ‘Yan Kasa Da Shekara 15 Ta Saka Dan Cristiano Ronaldo A Jerin ‘Yan Wasanta

Next Post

Jami’an tsaro ne ke jawo jama’a cikin aikata miyagun Laifuka: Gwamnan Borno, kalli dalilinsa

aksam

aksam

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa
Uncategorized

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

by aksam
June 15, 2026
Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato
Uncategorized

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

by aksam
June 2, 2026
Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa
Uncategorized

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

by aksam
May 31, 2026
Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya
Uncategorized

Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya

by aksam
May 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Rundunar  ‘Yan Sanda  Reshin Jihar Gombe Ta Dawo Da Dokar Hana Zirga Zirgar Babura A Jihar

Rundunar ‘Yan Sanda Reshin Jihar Gombe Ta Dawo Da Dokar Hana Zirga Zirgar Babura A Jihar

April 2, 2026
Yadda wani pasto ke amfani da matsayin sa wajen yiwa mabiyan sa fyaɗe

Yadda wani pasto ke amfani da matsayin sa wajen yiwa mabiyan sa fyaɗe

January 8, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media