A cewarsa, sakamakon jarabawar bana ya nuna yadda hukumar JAMB ta ƙara ƙaimi wajen inganta tsarin rubuta jarabawa, musamman ta hanyar amfani da kwamfuta wato CBT, da kuma hana duk wani yunƙurin satar amsa da ɗalibai ke yi a baya.
Alausa ya bayyana haka ne yayin wata tattaunawa da gidan talabijin na Channels TV a ranar Talata.
Ya ce a maimakon mutane su ɗauki wannan sakamako a matsayin koma-baya ga ilimi, ya kamata a fahimci cewa waɗanda suka samu sakamako mai kyau sun cancanta ne kuma sun yi jarabawa da gaskiya da riƙon amana
A ranar Litinin ne hukumar JAMB ta bayyana cewa daga cikin ɗalibai miliyan 1.95 da suka zauna jarabawar bana, kusan miliyan 1.53 — wato kashi 78 cikin 100 — ba su samu maki 200 ba.
Sai dai ɗalibai 12,414 kacal suka samu maki 300 ko sama da haka.
Ministan ya jaddada cewa wannan mataki na hana satar amsa zai taimaka wajen samar da ƙaimi na ɗalibai masu ƙwazo da amana, tare da ƙarfafa ingancin ilimi a Nijeriya.












