Gwamnatin Tarayya ta sanya mai shiga tsakani, Tukur Mamu, da Simon Ekpa tare da wasu mutane da kungiyoyi 47 a cikin jerin takunkumi bisa zargin hannu a daukar nauyin ta’addanci da kuma wasu ayyuka masu alaka da hakan.
Daga cikin wadanda aka ambata akwai Abdulsamat Ohida, wanda aka bayyana a matsayin babban kwamanda na kungiyar ISWAP a yankin Okene.
A cikin sabon jerin da kwamitin sanya takunkumi ya wallafa a shafinsa na intanet a ranar Asabar, gwamnati ta danganta Ohida da harin ranar 5 ga Yuni, 2022, da aka kai kan Cocin Katolika ta St. Francis da ke Owo a Jihar Ondo, da kuma harin da aka kai gidan gyaran hali na Kuje a ranar 5 ga Yuli, 2022.
Haka kuma, an saka sunan Mohammed Sani, wanda aka ce memba ne na kungiyar Ansarul Muslimina Fi Biladissudam (ANSARU), wata kungiya da ke da alaka da Al-Qaeda a yankin Maghreb na Afirka.
A cewar gwamnati, Sani ya samu horo karkashin Muktar Belmokhtar, wanda aka fi sani da lakabin “One Eyed,” inda ya kware wajen kirkirar hanyoyin sadarwa na sirri da kuma na’urorin fashewa na hannu.
An kuma bayyana shi a matsayin mai isar da sakonni da jagoran tafiye-tafiye ga mayakan AQIM a kasashen Aljeriya da Mali, kuma an ruwaito cewa ya tsere yayin fasa gidan yari na Kuje a watan Yulin 2022.
Sannan an kuma ambaci Abdurrahman Abdurrahman, wani babban kwamanda na ISWAP a Okene, cikin jerin.










