Mataimakin Shugaban Amurka, JD Vance, ya bayyana cewa Iran da Amurka sun kasa cimma matsaya kan kawo karshen yakin da ke faruwa a Gabas ta Tsakiya, bayan doguwar tattaunawa da aka yi a birnin Islamabad
Vance ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, inda ya kara da cewa ya bar taron bayan ya mika wa Tehran “tayin karshe kuma mafi inganci” daga bangaren Amurka.
Ya ce Washington na neman “tabbataccen alkawari” daga Iran cewa ba za ta kera makamin nukiliya ba, amma ya nuna rashin gamsuwa da cewa har yanzu ba a samu irin wannan tabbaci ba, duk da cewa wannan shi ne ganawa mafi girma tsakanin bangarorin biyu tun bayan juyin juya halin Musulunci na shekarar 1979.
Sai dai Vance ya nuna cewa har yanzu Amurka na bai wa Iran lokaci domin ta yi nazari kan tayin da aka gabatar mata.
A gefe guda kuma, Amurka ta sanar a ranar Talata cewa za ta dakatar da hare-hare tare da Isra’ila na tsawon makonni biyu, domin ba da damar ci gaba da tattaunawa.












