• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Gwamnatin Najeriya Taja Hankalin ‘Yan Najeriya Mazauna Iran Da Kasashen Larabawa

aksam by aksam
February 28, 2026
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Daga: Hassan Umar Gwammaja

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bukaci daukacin ‘yan Najeriya dake zaune a kasar Iran da sauran kasashen yankin tekun fasha (Gulf) da su kasance cikin tsananin sa ido da kiyaye kai, biyo bayan takun-saka da hare-haren soji da suka barke a yankin.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar a ranar Asabar, 28 ga Fabrairu, 2026, wadda kakakin ma’aikatar, Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya sanya wa hannu, gwamnatin ta bayyana cewa tana sanya idanu sosai kan yadda al’amura ke sauyawa bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai kan wasu wurare a Iran, da kuma martanin da ita ma Iran din ta mayar.

Don tabbatar da tsira da lafiyar ‘yan kasa, ma’aikatar ta fitar da wasu shawarwari guda biyar (5) kamar haka:-
* Gwamnati ta shawarci ‘yan Najeriya da su guji zirga-zirga a kusa da sansanonin soji, gine-ginen gwamnati, ko wuraren da ake ganin za su iya zama matattarar rikici.

* An bukaci mutane da su zauna a gida muddin ba wata muhimmiyar bukata ce ta fitar da su ba, sannan su guji shiga taron jama’a ko zanga-zanga.

* An bukaci ‘yan kasa da su kiyaye dukkan dokoki da matakan tsaro da hukumomin kasashen da suke ciki suka gindaya.

* Ma’aikatar ta bukaci mutane da su rinka sauraron kafafen yada labarai na kasa da kasa masu gaskiya, sannan su kiyayi yada labaran bogi.

* Sanarwar ta tabbatar da cewa ofisoshin jakadancin Najeriya da ke Tehran (Iran), Qatar, Bahrain, Kuwait, Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE), da Saudi Arabiya suna cikin shirin ko-ta-kwana don tallafa wa duk wani dan Najeriya da ya shiga cikin matsala.

A karshe, Gwamnatin Najeriya ta yi kira ga daukacin bangarorin da rikicin ya shafa da su kwantar da hankalinsu, su ajiye makamai su koma kan teburin tattaunawa domin samar da zaman lafiya a duniya.

Ta kuma sake jaddada cewa kare rayukan ‘yan Najeriya a duk inda suke a fadin duniya shi ne babban burin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

The Ghana Tourism Authority Paid a Working Visit To Assess The Usability Of The Paragliding landing Site in Kwahu West Ahead of This Year’s Easter Festivities

Next Post

Majalisar Leƙen Asiri ta Amurka ta ce ko da an yi gangamin yaƙi a kan Iran ba lalle ne a Iya murƙushe sojojin ƙasar da mulkin addini ba

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Makarantar Bara’u Ibrahim Memorial Ta Yi  Walimar Saukar Karatun Al’qur’ani Mai Girma Tare Da Bada Kyaututuka  Ga Dalibanta

Makarantar Bara’u Ibrahim Memorial Ta Yi Walimar Saukar Karatun Al’qur’ani Mai Girma Tare Da Bada Kyaututuka Ga Dalibanta

July 30, 2024

The Evolution of Online Slots: Navigating Payout Opportunities in a Dynamic Industry

April 23, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media