Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya umarci Hukumar Shige da Fice ta Najeriya (NIS) da ta gaggauta janye tare da dakatar da duk wasu fasfo da ke hannun mutanen da suka yi watsi da ɗan ƙasar Najeriya a hukumance.
Wannan umarni ya shafi ‘yan Najeriya da bukatunsu na yin watsi da ƙasa suka samu amincewar Shugaban Ƙasa, inda aka hana su ci gaba da riƙe ko amfani da takardun tafiye-tafiye na Najeriya bayan an kammala wannan tsari.
Mai ba Ministan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Alao Babatunde, ya bayyana a ranar Juma’a cewa ministan ya dogara da Sashe na 29, ƙananan sassa na (1) da (2) na Kundin Tsarin Mulki na shekarar 1999 (da aka yi wa gyara), wanda ya tanadi cewa: duk wani ɗan Najeriya baligi da ke son yin watsi da ƙasarsa zai gabatar da sanarwa bisa ƙa’ida.
Haka kuma, kundin ya ce Shugaban Ƙasa zai tabbatar da rajistar wannan sanarwa, kuma da zarar an yi hakan, mutumin zai daina kasancewa ɗan ƙasar Najeriya.
Tunji-Ojo ya jaddada cewa da zarar mutum ya rasa ɗan ƙasar Najeriya, ba shi da hurumin riƙe duk wata takardar hukuma ta ƙasa, ciki har da fasfo.
Wannan mataki na daga cikin jerin sauye-sauyen da Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida ke aiwatarwa kan fasfo da biza a ‘yan shekarun nan. Ministan ya bayyana cewa manufar hakan ita ce ƙarfafa tsaron iyakokin ƙasa, daƙile zamba ta amfani da bayanan sirri, da kuma kare martabar ɗan ƙasar Najeriya.
Ya ce, “Za mu ci gaba da ƙarfafa tsarin da zai kare iyakokin Najeriya, ya hana zamba ta bayanan sirri, ya kare darajar ɗan ƙasa, tare da sauƙaƙa sahihin tafiye-tafiye yayin da ake hana waɗanda ba su cancanta ba samun damar shiga.”












