Masu zanga-zanga sun kutsa kai babbar hedkwatar APC da ke Abuja kan batun dakatar da shugaban jam’iyya na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje
Sun buƙaci a soke duk wani mataki da Ganduje ya ɗauka bayan dakatar da shi kuma sun aike da saƙo ga shugaban ƙasa Tinubu
A cewarsu, zaman Ganduje a wannan kujera barazana ce babba ga zaɓen fitar da ɗan takarar da za a yi a Ondo ranar Asabar
Dandazon mambobin na APC sun ɗaga kwalaye da bana masu ɗauke da rubutu daban-daban, daga ciki sun ɓukaci Dakta Ganduje ya haƙura da shugabancin APC.
Ƙorafin da suka rubuta da nufin ya isa ga shugaban ƙasa ya samu sa hannun jagororin masu zanga-zangar, Denesi Momoh, Abdulkadir Shu’aibu da Adeyeye Olugbenga.
“Yallabai, yana da kyau mu ceci babbar jam’iyyarmu daga faɗawa matsala, ta hanyar tabbatar da soke duk wani mataki da aka dauka tun bayan dakatar da shugaban jam’iyya na ƙasa.










