Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa an ba wa Kamfanin Dangote izini na zama shi kaɗai mai samar da man jirgin sama, ko Jet A1, ga kamfanonin jiragen sama da ke aiki a kasar nan
Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya bayyana hakan a wata hira da aka watsa a tashar Channels TV ranar Talata, 8 ga watan Oktoba.
A cewar Keyamo, kamfanonin jiragen sama sun amince da Kamfanin Dangote mai samar da ganga 650,000 na mai a kowacce rana, a matsayin kadai mai samar musu da man jirgin sama, tare da amincewarsa da hadin kansa.
“Kamfanonin jiragen sama sun yi taro kwanan nan. Da yardata, wannan shawarar daga kamfanonin jiragen sama na Najeriya ce, cewa ya kamata su sayi Jet A1 daga kamfanin Dangote kaɗai.
“Kuna iya ganin cewa jiya muka fara sayen mai da Dangote da Naira. Duka Naira ne, babu wani ɓangare na dala,” inji Keyamo.
Ya bayyana cewa lokacin ya dace saboda Dangote da gwamnatin tarayya kwanan nan suka fara aiwatar da yarjejeniyar sayen mai da Naira.
Ya bayyana cewa wannan tsarin zai rage nauyin da aka sanya kan kuɗaɗen ƙasashen waje.
“Farashin ba zai kasance karkashin tasirin kasuwar duniya ba, ko kuma tasirin hauhawar farashin mai a kasuwar duniya. Zai kasance cikin kudin gida don mu san daidai farashinsa. Za mu saya cikin Naira. Ina da tabbacin cewa za mu samu Jet A1 mai rahusa,” inji Keyamo.










