Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi wa shugaban jam’iyyar APC mai mulki na ƙasa, Abdullahi Ganduje tayin muƙamin jakada a kowace kasa ta Afrika, kamar yadda sahihan majiyoyi su ka bayyana.
Jaridar DAILY Nigerian ta ce majiyoyi masu tushe wadanda su ka buƙaci a sakaya sunayensu sun tabbatar mata da cewa Tinubu ya fara wakilta Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio ya isar da “mummunan labarin” ga Ganduje.
A cewar majiyoyin, Akpabio ya shaida wa Ganduje cewa tayin muƙamin ambasada da Tinubu ya yi masa wata dabara ce ta kare shi daga shari’o’i na cin hanci da rashawa da ya ke fuskanta a Kano a halin yanzu.
Ganduje, wanda faifan bidiyonsa na cin hanci da rashawa a 2018 ya janyo masa ba’a da tsokana, yana fuskantar tuhume-tuhume na cin hanci da rashawa tare da matarsa, dansa da sauran masu hannu da shuni na sama da Naira biliyan 50 a jihar Kano.
Sai dai wasu majiyoyi na cikin gida sun ce Ganduje ya yi gunaguni kuma ya yi watsi da tayin shugaban kasar, inda ya bayyana cewa tuhumar da ake yi masa “ba mai dorewa ba ce” kuma zai ci nasara a shari’arsa a kotu.
“Duk irin goyon bayan da na yi wa shugaban kasa, sakaiyar da zai min kenan? ban da haka, na tsufa da yawa da zan je wata ƙasa a matsayin jakadanci. Duk tuhume-tuhumen da ake yi na karya ne, kuma zan ci nasara a shari’a ta a kotu,” an jiyo Ganduje yayin da ya ke mayar da martani ga Akpabio.
A cewar majiyoyin, daga baya shugaban kasar ya sanar da Ganduje shirin diflomasiyya tare da ba shi zabin “kowace kasa a Afirka”
Sai dai wasu majiyoyi sun ce shugaban ya yi masa zabi uku a Afirka, Asiya da Nahiyar Turai.
Amma kuma wasu majiyoyin sun baiyana cewa shi Tinubu ya fi son ya tura Ganduje a kasar Chadi a matsayin jakada, inda ta kara da cewa “babu wata kasa da ta san ciwon kanta a Nahiyar Turai da Asia da za ta karbi Ganduje a matsayin jakada idan aka yi duba da dumbin tuhume-tuhume na cin hanci a kan sa”.
Sai dai kuma majiyoyin sun tabbatar da cewa Ganduje ya dage sai ya riƙe muƙamin sa na shugaban jam’iyya, inda aka ce ya na ta kai gwauro ya kai mari wajen manyan makudantan Tinubu, irin su Bisi Akande domin su taushi shugaban kasa ya janye wannan kuduri na sa.












