Ƴan Najeriya dubu 5 ne suka mutu a shekara guda na mulkin Tinubu
Wani bincike da kafafen yada labarai na Najeriya da kungiyoyi suka gudanar ya nuna cewa ayyukan ta’addanci sun hallaka mutane 4,500 yayin da aka yi garkuwa da wasu dubu 7 cikin shekara guda tak karkashin mulkin Bola Ahmad Tinubu.
Yayin jawabinsa na ranar 29 ga watan Mayun bara lokacin da aka rantsar da shi, shugaban na Najeriya ya sha alwashin tunkarar matsalolin ta’addanci da kuma rashin tsaro gadan-gadan.
Wannan ba shi ne karon farko da shugaban ke yiwa ‘yan Najeriya alkawari kan magance matsalar tsaro ba, don kuwa ya kasance cikin manyan batutuwan da yake nanatawa a wajen yakin neman zabe.
To sai dai, shekara guda bayan darewarsa karagar mulki, a iya cewa babu wani sauyi na azo a gani a bangaren tsaro, illa ma dai sake sabon salon kai hare-hare da ‘yan bindiga musamman a arewacin kasar suke dauka, yayinda kungiyar Boko Haram tsagin Ansaru ke ci gaba da samun karfi.
Cikin makon da ya gabata sai dai kungiyar ta yi garkuwa da mutane 160 a jihar Neja, a wani hari da ba’a taba ganin irinsa a jihar ba.
Kungiyar ACLED mai tattara kididdigar kisa ko kuma mutanen da aka yi garkuwa da su ta ce bayananta sun nuna cewa mutane 4,556 ne suka rasa rayukansu sai wasu 7,086 da aka yi garkuwa da su a tsakanin ranakun 29 ga watan Mayun bara zuwa 11 ga watan Mayun da muke ciki.
Duk da alwakurran da shugaban yayi, da kuma ikirarin yaki da ta’addanci da manyan hafsoshin tsaron kasar keyi na yaki da ta’addanci, har yanzu matsalolin rashin tsaro na ci gaba da zama kanun labarai a gidajen jaridu.









