CDS Christopher Musa ya sha alwashin tona asirin duk wanda ya gano da hannu a harƙallar miyagun kwayoyi a Najeriya
Babban hafsan tsaron ya ɗauki wannan alƙawarin ne yayin ganawa da shugaban hukumar yaki da sha da fataucin Miyagun Kwayoyi ta kasa NDLEA, Buba Marwa a Abuja ranar Litinin
Ya kuma ƙara bai wa hukumar NDLEA tabbacin cewa rundunar soji za ta ci gaba da taimakawa wajen kawo karshen ta’amali da kwayoyi
CDS Musa ya kuma baiwa hukumar NDLEA tabbacin cewa zai taimaka wajen bankado masu safarar miyagun kwayoyi da masu cin zarafi.
Wannan dai shi ne karo na farko da babban hafsan tsaro da shugaban NDLEA, Manjo Janar Buba Marwa mai ritaya, suka haɗu suka tattauna a hukumance.










