Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya sulhunta Ministan Abuja Nyesom Wike da gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara kan rashin jituwar da ta yi kamari a tsakanin su.
Tsagin Wike ya amince da janye duk wani shiri na tsige gwamnan daga kan kujerar sa.
Tsagin gwamnan ya amince da janye duk wata shari’a da ya shigar gaban kotu.
Sannan bangarorin biyu sun amince da Shugabancin Amawhule a matsayin kakakin majalisar dokokin jihar Ribas, wanda kuma shine ya jagoranci yan majalisar nan 26 suka sauya sheka zuwa jam’iyyar APC daga PDP.
Kazalika Nyesom Wike da gwamna Fubara sun saka hannu kan Yarjejeniyar sulhu a gaban Shugaban Kasa, Bola Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima da shugaban Ma’aikatan fadar Shugaban Kasa, Hon Femi Gbajabiamila da tsaffin gwamnonin Jihar biyu da kuma sarakunan gargajiya na jihar.
By ABDULMUMIN tsayawa











