• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Batun zanga-zangar lumana, Kungiyar NLC tayi zazzafan martani ga hukumar DSS

aksam by aksam
February 22, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
468
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta sanar da cewa babu gudu babu ja da baya dangane da zanga-zangar gama-gari da za ta gudanar a ranar 27 da 28 ga wannan wata na Fabarairu.

Sanarwar dai martani ce ga Hukumar Tsaron Farin Kaya (DSS)da ta bukaci kungiyar kwadagon ta sauya tunani kan zanga-zangar da a cewarta babu lallai ta wanye lafiya ba.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Idan ba a manta ba a safiyar ranar Larabar ne hukumar tsaro ta Farin Kaya DSS ta yi jankunne ga kungiyar kwadagon da ta jingine shirinta na gudanar da zanga-zanga domin ci gaba da wanzuwar zaman lafiya da walwalar jama’a.

Gargadin DSS na zuwa ne tun bayan da a Juma’ar da ta gabata, NLC ta ayyana zanga-zangar kwanaki 2 a fadin kasar nan kan halin matsin da ‘yan Najeriya ke fuskanta da kuma matsalar tabarbarewar harkokin tsaro a fadin kasar.

Sai dai a wata sanarwa da mai magana da yawunta, Peter Afunanya ya fitar, DSS ta bukaci bangaren ‘yan kwadagon ya bi tafarkin tattaunawa a maimakon hanyoyin daka iya kara yamutsa hazo.

Sanarwar ta kara da cewar gwamnatoci a dukkanin matakai na iya bakin kokarinsu wajen rage radadin halin kuncin da ake ciki, don haka ya kamata a kyautata musu zato.

Sai dai da ya ke martani kan wannan gargadi na DSS, Shugaban NLC Joe Ajaero, ya ce maimakon yi wa kungiyarsu barazana, kamata ya yi DSS ta daura damarar kama duk wadanda za su kawo hargitsi a yayin zanga-zangar.

A cewar Kwamared Ajaero, tarihi ba zai taba yafe wa ƙungiyar ƙwadago ba ma damar ta zauna ta yi shiru kuma ta nade hannu alhali ’yan Najeriya na ci gaba da fuskantar tsadar rayuwa ba.

Shugaban kungiyar kwadagon, wanda ya bayyana matakin da ke tafe a matsayin “zanga-zangar lumana kan tsadar rayuwa da ba za a lamunta ba,” ya kara da cewa kungiyar kwadagon ba za ta nade hannunta ba yayin da ‘yan Najeriya ke ci gaba da rayuwa cikin kunci.

“Muna so DSS ta sani cewa babu inda aka taba samun tashin hankula a zanga-zagar lumana da kungiyar kwadago ta taba gudanarwa, don haka batun mu janye wannan bai taso ba.”

Shugaban NLC ya koka kan yadda tattalin arzikin kasar ya tabarbare yana mai cewa yanzu haka darajar naira ta kara kundunbala inda farashinta a kasuwar canjin kudi ya kai N1,900 kan kowacce dalar Amurka daya.

Ya ba da tabbacin cewa babu wanda ya ke son ci gaban Najeriya kamar kungiyar kwadago kuma ba za ta taba yin wani abu da zai jawo rashin zaman lafiya ba.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Zargin samadafadi na 10bn, EFCC zata gurfanar da wani tsohon gwamna a gaban kotu

Next Post

Tunanin al’ummar kasar sa, shugaban kasar Niger yayi wa Shinkafa farashi a fadin kasar

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Gwamnatin tarayya ta fadi dalilin da ya hana ɗalibai cin jarabawar JAMB

Gwamnatin tarayya ta fadi dalilin da ya hana ɗalibai cin jarabawar JAMB

May 7, 2025
Kungiyar PENGASSAN ta dauki doka a hannunta tsakanin ta da matatar Dangote

Kungiyar PENGASSAN ta dauki doka a hannunta tsakanin ta da matatar Dangote

September 30, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026
Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

Masu Zuba Jari 40+ daga Masar na Sha’awar Zuba Jari A Najeriya

August 23, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media