Hukumar EFCC mai yaki da rashin gaskiya za ta gurfanar da Abdulfattah Ahmed a kotu bisa zargin da ake yi masa.
Jaridar Punch ta bayyana cewa, a ranar Juma’ar nan mai zuwa EFCC za ta fara shari’a da Abdulfattah Ahmed a kotun tarayya.
Wata majiya ta shaida cewa za a kai karar tsohon gwamnan ne a babban kotun tarayya da ke birnin Ilorin a jihar Kwara.
“A ranar Juma’a za a gurfanar da shi a kotun tarayya da ke Ilorin bisa zargin karkatar da dukiyar da ta kai N10bn” –
Majiya daga EFCC tace EFCC: ta tsare tsohon gwamnan Kwara Tun ranar Litinin ‘dan siyasar yake tsare a hannun hukumar, ana da labarin ya fara kokawa kan halin da ya tsinci kan shi.
Ahmed ya yi zargin an hana shi ganin likitoci, lauyoyi da kuma masu girka abinci. Gayyatar hukumar EFCC ta canza salo Alhaji AbdulWahab Oba wanda shi ne sakataren yada labaran tsohon gwamnan ya ce EFCC ta gayyace shi ne sai ya je ofishinta.










