Kungiyar Matasan Lauyoyin Arewacin Najeriya, ta goyi bayan zanga-zangar lumana na tsadar rayuwa a Nijeriya.
Kungiyar Lauyoyin tayi kira ga Supeto Janar na ƴan sanda Najeriya da yayi kokarin kare da bada kariya ga masu zanga-zangar lumana kamar yadda sashe na 40 na kudin tsarin mulkin Najeriya ya tanadar.
“Mu gungun matasa ne na Lauyoyin da suka damu da miradun Arewacin Najeriya, da manufar tabbatar da dimokuradiyya cikin al’ummar.”
Mun yi wannan rubutun ne dangane da zanga-zangar lumana da za a fara a ranar 1 ga watan Agusta mai zuwa 2024, da kuma yin kira ga ‘yan sandan Najeriya su bi al’adar ƙasa-da-ƙasa ta hanyar kiyaye ka’idojin dokokin kare hakkin bil’adama a faɗin Najeriya.

Dokokin Kasashen duniya ya ba Ƴan ƙasa damar yin zanga-zangar lumana, kamar yadda yake a cikin sashe na 20 na Yarjejeniyar Kare Haƙƙin Bil Adama ta Duniya (UDHR), sashe na 21 da 22 na Yarjejeniya Ta Duniya kan Haƙƙin Bil Adama da Siyasa (ICCPR). Baya ga haka, sashe na 40 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya ya baiwa ‘yan Najeriya damar yin taron bayyana ra’ayoyinsu game da manufofin gwamnati da ayyukan da za su iya jefa rayuwar ƴan ƙasa cikin matsi da ƙunci.
Nijeriya na tafiyar da tsarin dimokuradiyyar ta a tafarkin dokoki. Hakan na nuni da cewa ofishin da kake ciki doka ce ta samar da ita kuma take ba ka kariya, don girmama hakan, ya zama wajibi ka tabbatar da cewa jami’anka sun gudanar da ayyukansu kamar yadda kundin tsarin mulkin Najeriya ya tanada da kuma al’adar duniya a lokacin zanga-zangar lumana.

Muna kira tare da baka shawara da kai da kayi nazari akan hukunci da kotun ECOWAS tayi a shari’ar EndSars na OBIANUJU CATHERINE UDEH & 2 Ors V FEDERAL REPUBLIC OF NIGERIA, inda kotun ta yi watsi da hujjojin da gwamnatin Najeriya ta gabatar, ta kuma umarci gwamnati da ta yi aiki da abin da ya rataya a wuyanta a karkashin Yarjejeniyar Afirka na Hakkokin Dan Adam da Jama’a, suyi bincike tareda gurfanar da jami’an tsaronta da ke da hannu dumu-dumu gurin aikata laifin, daga karshe kotun ta umarci gwamnati da ta biya kowannen su Naira miliyan 2 saboda tauye hakkinsu.
A karshe muna fatan zaka kare tare da tabbatar da haƙƙin ƴan ƙasa da yiwa doka biyayya.












