Babban Kwanturolan hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi, ya ce Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umurci hukumar da ta mayar da dukkan hatsin da aka kama ga masu su domin ci gaba da sayarwa a kasuwannin Najeriya.
Kwanturolan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron masu ruwa da tsaki a garin Kwangwalam da ke kan iyaka da Nijar a ƙaramar hukumar Maiadua ta jihar Katsina ranar Asabar, 9 ga watan Maris 2024, cewar rahoton Daily
Ya ce shugaban ya bayar da wannan umarni ne a cikin gagarumin karamcinsa na tabbatar da cewa al’ummar ƙasar nan sun samu isasshen abincin da za su saya a farashi mai rahusa a kasuwanni.
Ya ce, duk da haka, mayar da kayan abincin da aka ƙwace ga masu su ya dogara ne kawai da sharaɗin cewa za a sayar da su a kasuwannin Najeriya, rahoton Nigerian Tribune ya tabbatar.
“Gaba ɗayan manufar ita ce inganta samar da abinci da kuma tabbatar da cewa ƴan Najeriya ba za su kasance cikin yunwa ba. Shugaban ƙasa na kallon wannan a matsayin ɗaya daga cikin dabarun da za su taimaka wajen magance matsalar ƙarancin abinci.









