• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Ƴan Najeriya Sama da Miliyan 1.9 Ne Su Ka Nemi Aikin Immigration da Fire Service A Ƙasa da Wata Ɗaya

aksam by aksam
August 11, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

Daga Hassan Umar Gwammaja
Allah ’yan Najeriya 1,911,141 ne suka nemi shiga aikin Hukumar Civil Defence, Correctional, Fire and Immigration Services Board (CDCFIB) kafin rufewar shafin neman aiki a ranar Litinin, 11 ga Agusta, 2025, kamar yadda PUNCH Online ta gano.

An samu matsalolin fasaha a daukar ma’aikatan na shekarar 2025, inda shafin ya rika katsewa, dalilin hakan ya sa aka dakatar da shi na wani lokaci.

An fara shirya fara wannan daukar aiki tun ranar 26 ga Yuni, amma daga baya aka dage zuwa 14 ga Yuli, sannan aka sake daga shi zuwa 21 ga Yuli.

Saboda haka, lokacin da aka tsara rufe shafin shi ne ranar 4 ga Agusta, 2025,amma sai aka kara mako guda zuwa Litinin, 11 ga Agusta.

Duk da wadannan matsaloli, alkaluman da ke shafin CDCFIB sun nuna cewa mutane 1,911,141 ne suka nemi aikin kafin rufe shafin.

A cewar alkaluman, jihohin da suka fi yawan masu nema sun hada da Kogi (116,162), Kaduna (114,536), da Benue (110,565), yayin da Bayelsa (11,669) da Lagos (14,216) suka fi karanci.

Jihohi biyar da suka fi yawan masu nema su ne Kogi, Kaduna, Benue, Kano, da Niger, wadanda suka samar da jimillar masu nema 510,174.

A bangaren wadanda suka fi karanci kuwa, Bayelsa (11,669), Lagos (14,216), Rivers (22,210), Ebonyi (23,601), da Delta (27,962) sun hada gaba daya da masu nema 99,658.

A halin yanzu, CDCFIB ta bayyana matakan da masu nema za su bi bayan kammala neman aiki na shekarar 2025 ga hukumar tsaro ta paramilitary.

A cikin wasu sakonni da ta wallafa a shafinta na X a ranar Litinin, hukumar ta gode wa masu nema tare da bayyana cewa za a tuntubi wadanda aka zaba cikin ’yan kwanaki masu zuwa, tare da umarni kan mataki na gaba.

Hukumar ta shawarci masu nema da su rika duba sakonnin imel da na waya akai-akai, tare da shiga shafin CDCFIB da kafafen sada zumunta don samun sabbin bayanai.

Ta ce: “An rufe shafin neman aiki ! An rufe shafin neman aiki na Civil Defence, Correctional, Fire and Immigration Services Board. Muna gode wa duk masu nema bisa sha’awar su da jajircewa wajen yi wa kasa hidima cikin kima, gaskiya, da alfahari.

“Mataki na gaba! Za a tuntubi wadanda aka zaba cikin ’yan kwanaki masu zuwa tare da karin bayani. Don Allah ku rika duba imel da sakonnin waya, kuma ku kasance kuna binciken shafin da kuma kafafen sada zumunta don samun muhimman bayanai.”

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Gwamnan Kano Ya Buƙaci Kwamishinan Ma’aikatar Jinƙai Da Rage Raɗaɗin Talauci Da Ya Kula Da Ma’aikatar Sufuri Na Wucin Gadi.

Next Post

NUJ da Gwamnatin Kano Sun Kafa Kungiyar Tsofaffin ‘Yan Jarida, a jihar Kano domin kara wayarwa da kananan ‘yan jarida kai dangane da aikinsu

aksam

aksam

RelatedPosts

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa
Uncategorized

Iyalan Janar Rabe sun Musanta Sanarwar Gwamnatin Katsina Kan Dalilin Mutuwarsa

by aksam
June 15, 2026
Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato
Uncategorized

Mahara Sun Kashe ’Yan Yawon Sallah Bakwai A Sakkwato

by aksam
June 2, 2026
Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa
Uncategorized

Rahotanni Daga Jihar Imo Sun Bayyana Cewa Wani Magoyin Bayan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Ya Rasa Ransa

by aksam
May 31, 2026
Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya
Uncategorized

Zafin Rana Ya Hallaka Mutum 16 A Indiya

by aksam
May 31, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Kungiyar Ohanaeze Ndigbo Da Takwararta Ta Datawan Arewa Sun Koka Kan Yawan Tafiye-Tafiyen Da Shugaba Tinubu; Ke Yi

Kungiyar Ohanaeze Ndigbo Da Takwararta Ta Datawan Arewa Sun Koka Kan Yawan Tafiye-Tafiyen Da Shugaba Tinubu; Ke Yi

February 2, 2024
DHQ: Sojoji da ‘Yan Ta’adda Sun Rasa Rayuka a Jihar Borno

DHQ: Sojoji da ‘Yan Ta’adda Sun Rasa Rayuka a Jihar Borno

April 9, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media