• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Kungiyar Ohanaeze Ndigbo Da Takwararta Ta Datawan Arewa Sun Koka Kan Yawan Tafiye-Tafiyen Da Shugaba Tinubu; Ke Yi

aksam by aksam
February 2, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home SIYASA
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA: HASSAN UMAR GWAMMAJA

Kungiyar Dattawan Arewacin Nijeriya da takwararta ta Ohanaeze Ndigbo mai kare muradun al’ummar Igbo da wasu kungiyoyin farar hula sun bayyana rashin jin dadinsu game da tafiya zuwa Paris da Shugaba Bola Ahmad Tinubu ya yi daidai lokacin da kasar ke fama da karuwar matsalar tsaro.

RelatedPosts

Daukar DanKwankwaso Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Gwamnan Kano A NDC Ya Jaho Ce-ce-ku-ce

An Kona Fastocin Peter Obi Da Kwankwaso A Jihar Kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

A ranar Laraba 24 ga Janairu ne Shugaba Tinubu ya tafi zuwa Faransa domin wata ziyara ta kashin kai.

Wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban, Ajuri Ngelale ya fitar gabanin tafiyar, ta ce Tinubu zai koma Nijeriya cikin makon farko na watan Fabarairu.

Sai dai kungiyoyin a hirarsu da jaridar Daily Trust sun koka cewa babu gaskiya cikin sanarwar tafiyar la’akari da yadda aka kira tafiyar ta “kashin kai”.

Matakin kungiyoyin na zuwa ne bayan da shi ma tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya soki Tinubu inda ya bayyana shakku game da makasudin tafiyar tasa zuwa Faransa yayin da ake fuskantar karuwar matsalar ‘yan bindiga da sauran matsalolin tsaro da ke ci gaba da ta’azzara.

Sai dai Fadar Shugaban Kasar ta ce duk da cewa Tinubu ba ya kasar, yana aiki tukuru domin kawo saukin matsalolin kuma yana bai wa hukumomin tsaro dukkanin goyon bayan da suke bukata domin samun nasara kan masu aikata miyagun laifuka da nufin fitar da Nijeriya daga halin rashin tsaron da take ciki.

Tinubu dai ya sa kafa ya fice daga kasar ya yin da ake tsokaci game da jerin hare-haren da aka kai a Filato da sace-sacen jama’a a Abuja, babban birnin kasar da kuma hari na baya-bayan nan na sace dalibai da malaman makaranta a jihar Ekiti da ke kudu maso yammacin Nijeriya.

Kungiyar Dattawan Arewacin Nijeriyar ta ce tafiyar ta Tinubu zuwa Faris a irin wannan yanayi da ake ciki a kasar manuniya ce cewa shugaban ya dukufa ne wajen cimma kudurorinsa na kashin kai a maimakon bai wa ‘yan Nijeriya kwarin gwiwa a lokacin da suke bukatar hakan.

Daraktan yada labarai na kungiyar, Abdulazeez Sulaiman ya ce kungiyar tana ganin matakin na shugaban kasar na tabbatar da damuwar da ake nunawa cewa Nijeriya ta fada cikin matsalar rashin shugabanci nagari da rashin nuna damuwa da tausayi.

A nata bangaren, kungiyar Ohanaeze Ndigbo ta yi allah-wadai da tafiyar ta Shugaba Tinubu zuwa Faris a halin tabarbarewar tsaro da sauran kalubale da ake ciki.

Babban sakataren kungiyar, Mazi Okechukwu Isiguzoro ya ce bulaguron da Tinubu ya yi na zuwa ne a lokacin da kasar ke fuskantar kalubalen tattalin arziki.

Isiguzoro ya yi kira ga Tinubu da ya yi wa yan Nijeriya bayani dalilin yin irin wadannan tafiye-tafiye.

Shi ma shugaban kungiyar tabbatar da jagoranci nagari, GGT, Mista Tunde Salman ya ce da alama Shugaba Tinubu ya bai wa wasu manyan jami’ai har da mataimakin shugaban kasa damar tafiyar da al’amuran.

Ya ba da misali da wani kwarya-kwaryan taro da aka shirya kan tsaro game da karuwar matsalar a Arewacin Nijeriya, inda mataimakin shugaban kasa da ministocin tsaro suka zama masu taka rawa sosai a taron.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

‘Yan Wasan Kwallon Najeriya (Eagles) Sun Kai Matakin Na Kusa Da Na Kashe Bayan Cin Da Suka Yi Wa Takwararta Ta Kasar Angola Da Ci 1-0 Mai Ban Wushi

Next Post

Babu Abu Mafi Muni Dake Saurin Jefa Wanda Ya Aikatashi A Cikin Wutar Jahanama Sama Da Yin Wa Wani Kazafi:- Limamin Masallacin Madina Sheikh Abdulmuhsin Bin Muhammad Alkasim

aksam

aksam

RelatedPosts

Daukar DanKwankwaso Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Gwamnan Kano A NDC Ya Jaho Ce-ce-ku-ce
SIYASA

Daukar DanKwankwaso Ya Zama Dan Takarar Mataimakin Gwamnan Kano A NDC Ya Jaho Ce-ce-ku-ce

by aksam
June 16, 2026
An Kona Fastocin Peter Obi  Da  Kwankwaso  A Jihar Kano
SIYASA

An Kona Fastocin Peter Obi Da Kwankwaso A Jihar Kano

by aksam
June 1, 2026
Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma  Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC)  A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar
SIYASA

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, Ya Koma Jam’iyyar National Democratic Congress (NDC) A Hukumance; Inda Ya Karɓi Katin Zama Mamba Na Jam’iyyar

by aksam
May 3, 2026
Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Umarci  Duk Masu Riƙe Da Mukaman Siyasa Dake Da Niyyar Tsayawa Takara Dasu Yi Murabus Kafin Ranar Juma’a 24 ga Watan Afrilu 2026
SIYASA

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed Ya Fice Daga Jam’iyar PDP

by aksam
May 2, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Matatun Mai na China Sun Nemi Man Iran Bayan Faduwar Farashi

Matatun Mai na China Sun Nemi Man Iran Bayan Faduwar Farashi

April 8, 2026
Ƴan Najeriya Sama da Miliyan 1.9 Ne Su Ka Nemi Aikin Immigration da Fire Service A Ƙasa da Wata Ɗaya

Ƴan Najeriya Sama da Miliyan 1.9 Ne Su Ka Nemi Aikin Immigration da Fire Service A Ƙasa da Wata Ɗaya

August 11, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media