Daga: Hassan Umar Gwammaja
A yau Alhamis, 1 ga watan Mayu ne masu asusun ajiya a Bankunan dake Najeriya za su fara biyan Naira 6 a matsayin kudin dukkan sakon da bankunan suka turo musu (SMS Transaction Alert).
Matakin ya biyo bayan kara kudin kira da kamfanonin sadarwar kasar suka yi, bayan gwamnatin tarayya ta sahale musu kara kashi hamsin cikin dari (50%), mafari kenan da kudin ya tashi daga Naira Hudu (N4) zuwa Naira Shida (N6) a kowanne sako daya.
Tuni Bankuna daban-daban suka aika wa abokan hulɗar su sakon Email, domin sanar musu sa sabon tsarin cirar kudin aika sakon, inda suka ce cajin lambobin kasashen waje zai haura wannan farashi.
Haka kuma Bankunan sun bayyana muhimmancin karbar irin wannan sakonni daga Bankunan da mutane suke hulɗa da su, domin samun damar kula da dukkan wata hada-hadar asusun nasu.
A karshe Bankunan sun shawarci waɗanda basa buƙatar karbar sakonnin, da su ziyarci shafukan su na Internet domin dakatar su dakatar.












