Mai magana da yawun hukumar, Dakta Fabian Benjamin, ya ce an ƙirƙiri shafin ne da nufin karɓar kuɗi daga hannun waɗanda suka gaza rubuta jarabawar, da sunan za a sake musu lokaci.
“Wasu marasa gaskiya na karɓar kuɗi har Naira 15,700 daga ɗalibai da zargin za su taimaka musu su sake jarabawa. Wannan ba gaskiya ba ne, zamba ce tsagwaronta,” in ji shi.
JAMB ta bayyana cewa ba ta da hannu a wannan aiki kuma ba ta da alaƙa da masu gudanar da shi. Haka kuma ta bukaci Sterling Bank da ta dauki matakin toshe asusun da ke karɓar kuɗin.
Ta ce tana aiki da jami’an tsaro domin kamo waɗanda ke da hannu a lamarin.
Dakta Benjamin ya ƙara da cewa JAMB ba ta sake wa ɗalibi lokaci na jarabawa idan gazawarsa ta faru ne sakamakon kuskurensa ko wani dalili da bai shafi hukumar ba.
Sai dai in an samu matsala wajen tantance shi ta hanyar biometric, kuma an tabbatar da sahihancin matsalar, JAMB za ta ba shi damar sake rubuta jarabawar kyauta.
“Babu wani kuɗi da JAMB ke karɓa bayan an kammala rajista. Don haka muna kira ga ɗalibai da su guji fadawa tarkon ’yan damfara,” in ji shi.
Ya kuma shawarci jama’a da su rika kai rahoton duk wata alamar damfara da suka fuskanta ga hukuma cikin gaggawa











