Akalla masallata biyu ne aka kashe yayin sallar Juma’a a Anguwar Makera karkashin garin Kwasakwasa da ke karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.
Kamar yadda jaridar Daily Trust ta rahoto, lamarin ya afku ne da misalin karfe 2:00 na rana a ranar Juma’a, 8 ga watan Maris.
Wani babba a garin, Hudu Kwasakwasa, wanda ya tabbatar da lamarin, ya ce ‘yan bindigar sun bude wuta akan masallata, rahoton Leadership.
“Masallata biyu da aka kashe suna cikin sauran Musulmai da aka kai wa hari a masallacin Juma’ar a Angwar Makera lokacin da ‘yan bindiga suka bude masu wuta sannan suka sace wasu a yau (Juma’a).
Ya ce mutane suna cikin raka’a ta biyu lokacin da aka farmake su, wanda hakan ya sa sauran mutane guduwa domin tsira da rayuwarsu.
Ya kara da cewa a ‘yan kwanaki da suka gabata, ‘yan bindigar sun sace kimanin mutane 9 a garin da ake kira Angwar Kanawa karkashin yankin Kwasakwasa.
Ya roki hukumomin da abin ya shafa da su kawo masu dauki, cewa ‘yan bindigar na ta farmakar garuruwansu hankali kwance












