• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda Sarki Aminu Da ‘Yan Sanda Suka Kwace Ni A Hannu Wasu Matasa:– Dan Majalisar NNPP

aksam by aksam
July 22, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home TSARO
ADVERTISEMENT
475
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA

Wasu gungun matasa sun yi wa dan majalisar dokokin jihar Kano Abdul-Majid Umar dukan tsiya a wani taron da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado-Bayero ya halarta a ranar Asabar.

RelatedPosts

Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

Jami’an EFCC Sun Cafke Jami’in Tsaro Kan Zargin Safarar Zinaren Naira Biliyan 4.4 A Kano

Rasha Na Kara Amfani da Aljeriya a Matsayin Cibiyar Ayyukan Sojinta a Afirka

Umar dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Gwale, wasu Matasa ‘yan mazabarsa ne suka kai masa hari a unguwar Goron Dutse.

Dan majalisar a ranar Litinin din nan ya ce sarki Aminu Ado Bayero da ‘yan sanda sune suka kwace shi daga hannun matasan.

Idan za a iya tunawa Aksam Media ta rawaito Aminu Ado-Bayero, a ranar Asabar din da ta gabata, ya halarci taron addu’o’i na shekara-shekara da ake yiwa kasa da kano domin neman zaman lafiya da kwanciyar hankali , wanda shugabannin darikar Tijjaniyya suka shirya a gidan Marigayi Sheikh Isyaku Rabiu da ke Goron Dutse, a karamar hukumar Gwale ta Jihar

Umar wanda ya zauna a gefen sarkin a wajen taron, amma matasan sun far masa ne jim kadan da barin wurin taron.

Kamar yadda jaridar Premium Times ta ruwaito, matasan sun zarge shi ne da goyon bayan kudirin tsige sarkin.

Rahotanni sun ce matasan sun raunata dan majalisar ne kafin ya tsere cikin motar ‘yan sanda da ke wajen taron.

Dan majalisar ya shaida wa sashen Hausa na BBC a ranar Litinin cewa, dubban magoya bayan sarkin ne suka kai masa hari bayan ya bar taron ba tare da sanin ya kamata ba.

Umar ya ce ya bar wurin ne a lokacin da ya lura da cewa wurin babu tsaro.

“Bayan da hambararren sarkin ya isa wurin taron, sai magoya bayansa suka fara zagina da abokan aikina, suna zargin mu da soke dokar majalisar masarautun 2019 da ta kai ga tsige Sarkin.

“Sarkin da aka tube ya tare wani daga cikin fadawansa da ya yi yunkurin buge ni. Sarkin da kansa ya yi amfani da hannunsa wajen tare dukan da bafaden ya kawo, ya kuma yi wa wani wanda ya sake yunkurin duka na tsawa,” in ji Mista Umar.

Umar ya ce ya yanke shawarar barin taron ne lokacin da ya lura cewa shi kadai ne jami’in gwamnati a wajen taron.

“Na kara shiga damuwa bayan na bar wurin taron yayin da mutane dauke da muggan makamai suka far min. Na yi sauri na shiga motar ‘yan sanda. Da haka aka kubutar da ni daga harin.

“Magoya bayana biyu sun jikkata lokacin da muke kokarin barin wurin taron”, in ji dan majalisar.

Sai dai daya daga cikin hadiman sarkin kan harkokin kafafen yada labarai, Khalid Uba Adamu ya musanta cewa matasan suna cikin tawagar sarkin.

Ya ce Sarki Aminu Ado Bayero ya isa wurin taron ne da dimbin magoya bayansa, amma babu daya daga cikinsu da ke dauke da makami.

Rikicin masarautar Kano ya fara ne bayan da ‘yan majalisar a ranar 23 ga Mayu, 2024 suka soke dokar majalisar masarautun jihar ta 2019, wadda tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje ya kirkiro sabbin masarautu hudu.

Share190Tweet119SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Dangote ya shirya sayar da matatar man fetur dinsa kan wani babban Dalili

Next Post

Shugabancin tashar Yankaba ya dauki matakin dakile yawaitar shaye-shayen miyagun kwayoyi a tashar

aksam

aksam

RelatedPosts

Rundunar  Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane
TSARO

Rundunar Sojin Najeriya Ta Yi Nasarar Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane

by aksam
June 16, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
TSARO

Jami’an EFCC Sun Cafke Jami’in Tsaro Kan Zargin Safarar Zinaren Naira Biliyan 4.4 A Kano

by aksam
June 13, 2026
Rasha Na Kara Amfani da Aljeriya a Matsayin Cibiyar Ayyukan Sojinta a Afirka
TSARO

Rasha Na Kara Amfani da Aljeriya a Matsayin Cibiyar Ayyukan Sojinta a Afirka

by Khadija Maitaya
June 6, 2026
Hukumar Civil Defense Ta Kori Ma’aikatan Ta Na Sa-Kai Su Biyar A Jihar Kano
TSARO

Hukumar Civil Defense Ta Kori Ma’aikatan Ta Na Sa-Kai Su Biyar A Jihar Kano

by aksam
June 2, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Hogyan Használj Bónuszkódot a ragnaro casinoban?

April 22, 2025

Zargin satar IPhone 12 pro da infinite note 10, wani matashi ya karbi rantsuwa a kotu Dan wanke kansa

May 3, 2024
ADVERTISEMENT

Trending.

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media