Daga Ibrahim S Gama
Shugaban Kungiyar Yankasuwa ta Amata dake tashar Yankaba ta jaddada aniyarta na Dakatar da masu rashin ayyukan yi a cikin Tashar domin dakile taammali da mugwan Kwayoyi a yankunan Tashar.
Shugaban Kungiyar Nasuru Muhammad ne ya jaddada hakan a lokacin da Kungiyar ta yaye wasu Matasa da suka ajiye Makamansu Wanda ya gudana a Tashar.
Nasuru Muhammad ya bai kamata a rika tsangwamayar yaran da suke aikata laifika marasa kyau bai,Wanda yin haka yana taka muhimmiyar rawa wajen lalacewarsu.
Shugaban Kungiyar ya yi kira Gwamnatoci da masu hannu da shuni da su rika zakulo irin wadan nan masu aikata laifika domin Neman musu ayyukan yi da su dauke hankulansu da aikata munanan dabiun da suke aikatawa.
A jawabinsa Shugaban jami’an sa kai na Tashar yankaba Alh Bala Danyalwa yace,akwai wani Kalubalen da ya kamata Gwamnatin Karamar Hukumar da ta jiha su sani,inda ya bayyana cewa, akwai yara kusan Dari biyar da suke Kwana a cikin Tashar yankaba wadanda ba,a San daga inda suka fito ba.
Yace, suna iya kokarinsu wajen mayar da wasu da suka San garuruwan iyayensu da jihohinsu Wanda sun mayar da yara da ba za su kirgu ba zuwa jihohinsu Wanda suna yi ne da aljihunsu.
Ya kuma bayyana cewa, nan gaba kadan Kungiyar za ta sake zakulo wasu Matasan da basu da ayyukan yi tare da basu horo akan sana’oi daban daban da ma basu jari.
Wani daga cikin Matasan da suka amfana da wannan tagomashi Muhammad Auwal sani ya godewa Shugabancin Kungiyar ta AMATA Yankaba, bisa jarin da aka bashi tare da Kayayyakin Wankin Mota domin ya dogara da Kawunansu.
Matashin Auwal sani, ya sha Alwashin yin amfani da Kudaden ta hanyar da suka kamata domin dogaro da kansa kamar yadda aka bukacesu,inda ya bayyana cewa, sun yi mutukar farin ciki tare da yin alkawarin ba za su sake aikata Munanan Dabi’u ba.











