AUREN JINSI: Ya kamata Malamai su rika yin bincike kafin suyi magana.
Sanatan Kano ta kudu Hon, Kawu Sumaila ya bayyana mamaki sa kan ruwawan hudubobi daga mabanbantan masallatan Juma’a da malamai suka gudanar a kan auren jinsi.
A cewar sa kamata ya yi su fara gudanar da bincike kamar yadda Alqur’ani ya koyar da musulmai akan wani labari idan yazo kafin a zartar masa da hukunci
“Nayi mamaki da irin hudubobin da naji malamai keyi alhali basu gabatar da bincike akan lamarin auren jinsi ba, ya kamata su rika girmama minbarin da suke kai su fara bincike kafin yin magana kamar yadda Alkur’ani yayi magana.












