A yayin da ake ta fama da matsalar tsaro a yankuna da dama na Najeriya ciki harda Abuja, yanzu haka an kama wasu bata garin jami’an ‘yan sanda bisa zargin su da karbar naira miliyan 29.9 da karfin tsiya daga hannun wani mazaunin birnin tarayya Abuja
Lamarin, a cewar Harrison Gwamnishu, dan takarar jam’iyyar Labour Party (LP) a zaben 2023, ya faru ne a watan Janairu.
Ya ce jami’an ‘yan sanda sun yi garkuwa da dan kasuwar ne a Abuja inda suka tsare shi tare da yi masa barazana har sai da ya tura musu dukkan kudaden da ke cikin asusun bankinsa.
Daga nan ne kuma suka tilasta shi ya kira ‘yan uwa da abokan arziki su ci gaba da aika masa kudi yana basu kafin su sake shi.
Ya kara da cewa ‘yan sandan sun kama mutumin ne ba tare da wani dalili ba, inda ya ce jami’an ‘yan sandan ba su nemi ya rubuta wani jawabi ba. Kana ya wallafa hotunan shaidar tura kudaden tare da bidiyon da ya wallafa.
Da yake tsokaci kan wannan bidiyo a ranar Talata, kakakin rundunar, yan sanda ta kasa Olumuyiwa Adejobi, ya tabbatar da kama wasu daga cikin masu laifin, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.











