DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Babbar Kotun Jihar Kano ta tabbatar da dakatarwar da aka yi wa Shugaban Jam’iyyar APC na Kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, daga jam’iyyar.
An dai dakatar da tsohon gwamnan Kano, Ganduje, daga Jam’iyyar APC ne a mazabarsa, kan zargin rashawa.
Cutar Zazzabi Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutune 45 A Kauyen Jihar Kano
A ranar Litinin ne dai shugabancin jam’iyyar na mazabar Ganduje suka sanar da dakatar da shi.
Amma daga bisani wani sashi na shugabancin jam’iyyar an kuma na jiha ya sanar da korar wadanda suka sanar da dakatar da Gandujen.
Kotun dai ta dage sauraron karar zuwa ranar 30 ga watan Afrilu, 2024.
Wannan dai na zuwa ne a ranar da hukumar yaki da rashawa ta jihar Kano ke sa ran gufanar da Ganduje da gaban kuliya kan zargin almundahana a zamanin mulkinsa a jihar.









