Daga Khadija Muhammad Maitaya.
Mataimakin Shugaban Ƙasa zai jagoranci tawaga zuwa Jamhuriyar Benin domin farfaɗo da masana’antar yadi
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, zai jagoranci gwamnoni shida da manyan jami’an gwamnatin tarayya zuwa Jamhuriyar Benin a yau Alhamis, domin nazarin hanyoyin farfaɗo da masana’antar yadi da bunƙasa masana’antun sarrafa amfanin gona a Najeriya.
Tawagar za ta kai ziyara Yankin Masana’antu na Glo-Djigbé da ke kusa da birnin Cotonou, inda za ta gana da jami’an gwamnatin Benin da masu zuba jari da kuma masu gudanar da masana’antu.
Ziyarar na da nufin nazarin yadda Benin ke tafiyar da masana’antun sarrafa auduga da yadi, tare da duba hanyoyin inganta tsarin sarrafa kayayyakin amfanin gona da jawo hannun jari.
Haka kuma, jami’an za su tattauna kan yadda za a haɗa manoman auduga, masana’antun sarrafa auduga, masana’antun yadi da kasuwannin fitar da kayayyaki zuwa ƙasashen waje, domin ƙarfafa sarkar samar da kayayyaki a cikin gida.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce wannan mataki zai taimaka wajen rage dogaro da shigo da yadudduka daga ƙasashen waje, adana kuɗaɗen musayar ƙasashen waje, tare da samar da dubban guraben ayyukan yi.










