• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yan bindiga sun sake kai sabon hari a jihar Katsina

aksam by aksam
April 17, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
467
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Ƴanbindiga sun kai samame a garin Na-Alma a yankin karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina , inda suka kona gidaje, suka kuma sace gomman mutane, galibi mata, har da masu juna biyu, da kananan yara, da wani wanda ‘yan bindiga suka taba sare wa hannu da kafa, bayan kashe wani mai unguwa.

Bayanai sun ce, hare-haren ‘yan bindigan na baya-bayan nan sun jefa mutane da dama cikin tasku.

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

Wani mutumin yankin, wanda ya tsallake rijiya da kundun baya ya ce suna cikin rudani, kuma kashi takwas cikin goma na mutanen garin sun yi kaura.

Mutumin ya kuma ce sun shaida wa jami’an tsaro cewa sun samu bayanan sirri na harin da ƴanbindigar za su kai garin nasu : ” Tun wajen takwas da rabi na dare muka shaida wa jami’an tsaro amman ba su zo ba har sai da mutanennan suka shiga suka fara harbi, sai dai kawai su ce ga su nan zuwa, amman ba su zo ba har sai da ƴanbindiga suka gama kone-kone da duk abin da za su yi sannan suka zo.”

Mutumin ya kara da cewa an yi masu gagarumin ta’adi a harin da ‘yanbindigan suka kai “Asarar kam Allah kadai Ya san yawanta saboda haka suka bi gida-gida suka ƙona kuma duk manyan gidaje ne suka kona sun kuma kashe mai-unguwa.”

Mutumin da muka sakaya sunansa ya ce maharan sun tafi da wani Alhaji da suka datse wa ƙafa da hannu kwanakin baya, sannan mata sun kai tara wadanda kowace na da goyo da kuma wasu masu ciki biyu, ” Idan aka hada da matan da yaran da wannan Alhajin za su kai mutum 20.”

Mutanen yankin sun ce suna fuskantar hare-haren ƴanbindiga fiye da kowane lokaci.

Kwamishinan tsaro na jihar Katsina, Dakta Nasiru Mu’azu ya danganta wannan hari da aka kai garin Na-Alma, da cewa hari ne irin na ramuwar gayya.

Sakamakon halaka wani mutum da ake zargin kasurgumin dan bindiga ne da mukarrabansa, wadanda suka addabi yankin karamar hukumar Malumfashi da kewayenta.

Kuma ana nan ana ci gaba da kokarin murkushe wannan matsala ta tsaro a dukkan wuraren da ake fama da ita a jihar ta Katsina, in ji shi.

Share187Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Uwar jam’iyyar APC ta kano ta dauki tsatstsauran mataki kan wadanda suka dakatar da Ganduje

Next Post

Wata Kotu Ta Tabbatar Da Dakatarwar Da Aka Yi Wa Ganduje Daga Shugaban Jam’iyyar APC

aksam

aksam

RelatedPosts

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa  ƴar Tik-tok  Dake Unguwar  Ɗanbare A Jihar Kano
LABARAI

Wani Matashi Ya Rasu A Gidan Budurwarsa ƴar Tik-tok Dake Unguwar Ɗanbare A Jihar Kano

by aksam
June 20, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro

by Khadija Maitaya
June 19, 2026
Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka
LABARAI

Sky News: Yaƙin Trump da Iran Na Daya Daga Cikin Manyan Kurakuran Dabarun Amurka

by Khadija Maitaya
June 16, 2026
China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI
LABARAI

China Ta Soke Darussa 12,000 na Jami’o’i Domin Shirin Zamani na AI

by Khadija Maitaya
June 14, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yadda Jirgin sama ɗauke da mutane 242 yayi hatsari

Yadda Jirgin sama ɗauke da mutane 242 yayi hatsari

June 12, 2025
Kungiyar Kwadago ta NLC Ta Dakatar Da Zanga-zangar Adawa Da Karin Farashin Kudin Kira Da Na Data

Kungiyar Kwadago ta NLC Ta Dakatar Da Zanga-zangar Adawa Da Karin Farashin Kudin Kira Da Na Data

February 3, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Ango Bulaye

June 12, 2026
An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

An Kammala Gasar Kwallon Kafar Sada Zumunchi Dan Muna Murnar Zagayuwar Sallah Babba Cikin Nasara A Garin Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 1, 2026
The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

The Emir of Zangon Nkawkawo, Alhaji Abdul-Nasir Usman, Extends Eid Greetings

June 1, 2026
Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da  Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma  A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

Irin Yadda Ake Cigaba Da Gudanar Da Karatun Saukar Al’qur’ani Mai Girma A Zango Nkawkawo Dake Kasar Ghana

June 5, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Sha’ibu Sani Mai Atamfa (Bulaye)

June 15, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media