Shugabancin Jam’iyyar APC na Jihar Kano ya Dakatar da Shugabannin Jam’iyyar na Mazaɓar Ganduje, waɗanda suka dakatar da Shugaban Jam’iyyar na ƙasa Abdullahi Umar Ganduje daga Jam’iyyar.
Shugaban Jam’iyyar na Jihar Kano Abdullahi Abbas ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya ce sun ɗauki matakin ne biyo bayan rahoton sirri da suka samu akan yadda shugabannin suka yi wata ganawar sirri da ɓangaren Adawa.
A cewar Abdullahi Abbas, “Muna da Hujjoji masu ƙarfi na yadda waɗancan Shugabanni da muka kora suka yi taro da Muƙarraban Gwamnatin Kano.
Shima Shugaban Jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Dawakin Tofa Inusa Dawanau ya shaidawa manema labarai cewar sun dakatar da dukkan waɗanda suke da hannu akan lamarin, a sakamakon kama su da da yunƙurin cin amanar Jam’iyyar ta hanyar yin taro da tsagin adawa.
Kwamitin ayyukan Jam’iyyar na jihar Kano ya ce Dakatarwar ta Watanni Shida ce domin a sami damar gudanar da bincike kan tarin Zarge-zargen da ake yi musu.
A ɗazu ne muka baku labarin yadda Shugabancin Jam’iyyar APC a Mazaɓar Ganduje dake ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ya dakatar da Shugaban Jam’iyyar na Ƙasa Dakta Abdullahi Umar Ganduje saboda zargin karɓar cin Hanci.












