Bayan wata ganawa da wakilan gwamnati a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya a daren Litinin, NLC ta yanke shawarar dakatar da zanga-zangar har sai an kammala tattaunawa.
Da yake magana da ‘yan jarida bayan taron, Shugaban NLC, Joe Ajaero, ya bayyana cewa gwamnati ta amince da kafa wani babban kwamiti don sake duba karin farashin kudin kira da na data da kamfanonin sadarwa ke shirin kaddamawa
A cewarsa, kwamitin zai ƙunshi wakilai biyar daga kowanne bangare, kuma ana sa ran zai gabatar da sakamakonsa cikin makonni biyu.












