DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta umurci dillalan magunguna dake kasuwar kasuwar Sabon Gari dake yankin Karamar Hukumar Fagge a Kano da su tashi nan take.
Baya ga haka, kotun ta kuma ba da umarnin mayar da masu sana’ar ta hada-hadar magunguna zuwa cibiyar da aka kebe don siyar da magunguna a Dangoro da ke kan titin Zariya a Kano
Alkalin Kotun Mai shari’a Simon Amobeda a hukuncin da ya yanke a ranar Juma’a ya yi watsi da karar da kungiyar masu hada-hadar magunguna ta Najeriya, da wasu mutane shida suka shiga saboda rashin cancanta.
Shugabancin kungiyar yan maganin na jihar Kano, sun ce za su magantu kan batun.











