Matashin ya taki rashin sa’a ne a kokarinsa na damfarar yan uwansa duk da cewar ya kitsa garkuwa da kansa
Rundunar yan sandan babban birnin tarayya ta kama mutumin kamar yadda ya bayyana a wata sanarwa da ta saki a ranar Asabar, 20 ga watan Janairu
SP Josephine Adeh, kakakin yan sandan ta kuma bayyana cewa rahotannin garkuwa da mutane a rukunin gidajen River Park ba gaskiya bane
A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, rundunar yan sandan FCT ta bayyana rahotannin a matsayin kanzon kurege sannan ta nanata cewa babu wanda aka sace a rukunin gidajen River Park.
A cewar rundunar, an kama Agu ne bayan ya kitsa garkuwa da kansa domin damfarar dan uwansa da yake zaune a rukunin gidajen. Sanarwar ta ce:
“Rundunar yan sandan FCT na sane da labaran da ke yawo game da zargin garkuwa da mutane a rukunin gidajen River Park a safiyar yau sannan tana fatan bayyana cewa sabanin rahotannin, babu wanda aka sace a rukunin gidajen River Park











