• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Yadda Kasar Jamus ta sassauta dokar zama dan kasa ga baki

aksam by aksam
January 21, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Majalisar Dokokin Jamus wato Bundestag ta amince da wata sabuwar doka da ta sassauta matakan bai wa baki ‘yan kasashen ketare zama ‘yan kasa.

Dokar ta rage shekarun mallakar fasfon daga takwas zuwa biyar.

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

Bayan an Jima ana kai ruwa rana a ranar Juma’ar da ta gabata, Majalisar Dokokin Jamus ta amince da bai wa wadanda suka shafe shekaru biyar a kasar fasfo na dan kasa, idan suka cika wasu ka’idojin a maimakon shekaru takwas zuwa goma.

Sanarwar dai ta jefa dubban mutane cikin yanayi na farin ciki, musamman wasu ‘yan kasashen Afirka da ke rayuwa a kasar.

To kashi goma sha takwas cikin dari na al’ummar Jamus dai baki ne kamar yadda kididdiga a kasar ta nunar, da dama daga cikin su sun shafe shekaru ba tare da sun sami takardar ba, saboda tsaurin matakan samun takardar.

Yanzu dai sabuwar dokar ta amince mutum ya ci gaba da amfani da fasfo na kasarsa ta asali, sabanın yadda a baya dokar ta Jamus ba ta yadda da hakan ba, idan har mutum bai fito daga Tarayyar Turai ba, amma kuma akwai kasashe kamar Ghana da Kamaru da dokar kasarsu ba ta amince musu zama ‘yan wata kasa baya ga kasar a lokaci guda ba.

Leo King dan Kamaru ya ce ‘’Duk da na ji dadin wannan labarin amma sai murna ta koma ciki gani na a matsayina na dan Kamaru kafin na ci gajiyar dokar sai na sallama fasfona na Kamaru, wanda hakan ya saka ni cikin bakin ciki, amma fatana naga gwamnatin Kamaru ta sake nazari ta sassauta matakinta don muma mu ci gajiyar tsarin na amfani da fasfon kasashen biyu tare.”

Bugu da kari dai, sabuwar dokar ta tanadi a bai wa wadanda suka cika shekaru uku a kasar katin dan kasa na dindirdin, musanman ga wadanda suka ba da himma a lakantar harshen Jamusanci da kuma sajewa da al’adun kasar.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Wani matashi ya shiga hanun jamian tsaro bayan da ya sa ayi garkuwa da shi a nemi kudin fansa a wajan yanuwan sa

Next Post

Yahudawa na zanga-zangar neman Netanyahu ya yi murabus daga shugaban kasar Isra’ila

aksam

aksam

RelatedPosts

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan
LABARAI

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf Ya Sanya Ranar Talata 05 GA watan Mayu 2026, A Matsayin Ranar Da Zai Jagoranci Rantsar Da Murtala Sule Garo A Matsayin Mataimakin Gwamnan

by aksam
May 4, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
LABARAI

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

by aksam
May 4, 2026
NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano
LABARAI

NDLEA Ta Kama Mutane 6, Ta Rushe Maboyar Miyagun Kwayoyi a BUK Old Site Kano

by Khadija Maitaya
May 4, 2026
Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A  Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga  Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC
LABARAI

Tsohon Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar Labour Party, Peter Obi, Ya Sanar Da Ficewarsa Daga Jam’iyyar Haɗaka Ya ADC

by aksam
May 3, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yakin palatine,  Dubban daliban jami’a sun gudanar da zanga-zanga  a Burtaniya

Yakin palatine, Dubban daliban jami’a sun gudanar da zanga-zanga a Burtaniya

October 21, 2023
Alamu Na Nuni Da Cewa;- Yan Zo Haka An Fara Bawa Wasu Daga Cikin Ma’ikatan KAECO Da Aka Kora Da Aiki Takardar Sallama

Alamu Na Nuni Da Cewa;- Yan Zo Haka An Fara Bawa Wasu Daga Cikin Ma’ikatan KAECO Da Aka Kora Da Aiki Takardar Sallama

February 4, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media