DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Kotun Shari’ar Musulunci Dake Zamanta a Daura Road, cikin garin Kaduna wace mai Shari’a Malam Mustapha Umar yake alkalanci ta karbi karar da: Sa’idu Abdulkarim mai shekara 38, wada yace shi Manomine, mazaunin garin birnin Yaro dake karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna, aka a dawomasa da tsabar Kudinsa naira milliyan daya da dubu dari uku da hamsin
Ranar lahadi 14 ga watan janairun wannan shekarane aka dauramusu aure da shi da Amaryarsa Sha’awanatu Musa Mai shekara 20, mazauniyar kasuwar magani dake cikin garin Kaduna, kwana daya da daura auren sai ta gudu, shi yasa na kawo kararta kotu domin ta dawo min kudadina da na kashe, in ji Ango Sa’idu
Alƙalin ya tambaye wace ake kara hakane ? tace hakane, amma satina daya a gidansa ba kwana daya ba, ya sake tambayarta ya maganar kudinsa ? sai tace ya samana kudin da ba za mu iya biya ba.
Anan Angon Sa’idu ya fito da takarda wace aka yi yarjijiniyar da iyanta da nasa za’a biyashi naira (800,000) a maimakon wacen kudi, duk da haka tace baza su iya biya ba. “Ma’ana basu da su” in ji Shawa’anatu
Sai Alkali Malam Mustapha Umar ya daga Shari’ar zuwa ranar 1 ga watan April, 2024










