DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Gwamnan jihar Ondo, Oluwarotimi Akeredolu, ya bukaci mataimakinsa, Lucky Aiyedatiwa, da ya dauki nauyinsa a matsayin mukaddashin gwamnan jahar Ondo yayin da ya tafi hutun jinya daga ranar Laraba.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa da kakakin gwamnan, Richard Olatunde ya fitar ranar Talata.
Sanarwar ta ce gwamnan, wanda ke fama da rashin lafiya tun daga watan Janairu, zai ba da fifiko ga lafiyarsa tare da tabbatar da samun cikakkiyar lafiya kafin ya ci gaba da aikinsa.
Wasu sassan sanarwar sun ce za mika wa majalisar dokokin jihar wata wasika ta hukuma dangane da hutun jinya da sanarwar mika mulki bisa ga kundin tsarin mulkin Najeriya.
A matsayinsa na Babban Lauyan Najeriya kuma dan Najeriya da ake girmama dokokin kasa Gwamna Akeredolu ya dade yana kyamar mika ragamar mulki ga mataimakinsa a lokacin hutun da yake yi na shekara.
Hakan yasa wani lokaci can baya shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kira wani taro tareda mataimakin gwamna da kuma wakilan gwamna Akerodolu inda ya baiwa mataimakin gwamna shawarar cewa ya cigaba da hakuri da matsayinsa na mataimaki har zuwa lokacin da gwamnan zai samu lafiya.












