DAGA HASSAN UMAR GWAMMAJA
Masani a fannin mulki da gudanarwa Dr. Sa’idu Ahmad Dukawa ya ce Majalisar Dokoki ta Kasa da ta jahohi suna da hurumin bincikar duk wani almari da ya shafi al’ummar kasa.
A yayin da wakilinmu ke ganawa da shi akan umarnin bincike da Majalisar Dokoki ta Kasa ta bayar akan gano dalilan dakatar da aikin hakar mai a Kalmani dake jahar Bauchi Dr. Dukawa ya ce ya zamo wajibi yin hakan domin gano wadanda ke yiwa al’amarin zagon kasa.
Akan batun binciken yanda aka kashe sojoji a Jahar Abia kuwa, Malamin Jami’ar Bayero Dr. Sa’idu Ahmad Dukawa ya ce yana da matukar muhimmanci Majalisar ta yi bincike da manufar samarwa jami’an tsaron kariya daga bata gari domin karfafa musu guiwa wajen sadaukar da akai a aikinsu kare kasa.
Haka kuma goyi bayan binciken tsohon gwamnan babban bankin kasa Godwin Emefele da takwaransa na jahar Kaduna Malam Nasir ElRufai da makamantansu domin karbo dukiyar da ake zargin sun warware tare da amfani da ita yanda yakamata ga al’umma.












