Daga: Hassan Umar Gwammaja
Ya bayyana hakane a ranar Lahadi nan, ya ce sakamakon zaben kananan hukumomin jihar ya kawo karshen cin zarafi da siyasar ubangida a jihar ta Ribas.
Atiku ya ce wannan zai da damar yi wa al’umma aiki yadda ya dace kuma damar bin kundin tsarin mulki a jihar.
Ya yabawa gwamna Sim Fubara na jihar a kan sakamakon zaben kananan hukumomin da aka kammala a jihar.
Atiku ya kuma ce sakamakon zaben ya nuna cewa Fubara, ya nuna jajircewarsa ga muradun jama’a da kuma kare martabar zaben kananan hukumomi.
Sanarwar da Atiku ya sanyawa hannu ta kuma kara da ce: “A yayin da aka kammala zaben kananan hukumomi a jihar, an kawo ƙarshen tsoratarwar da ake yi wa gwamnan, wanda hakan zai ya bayar da damar fara gudanar da kyakkyawan shugabanci a jihar.












