• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Shugaban Turkiya ya fadi Abin da ya kamata Rasha ta yi a kan Azerbaijan

aksam by aksam
July 5, 2025
Reading Time: 2 mins read
0
Home Uncategorized
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Shugaban ƙasar Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi kira ga Rasha da Azerbaijan su yi haƙuri da juna a yayin da ake samun ƙaruwar fargaba a tsakanin ƙasashen biyu, yana mai jaddada cewa Ankara tana da “dangantaka mai ƙarfi” da Moscow da Baku.

Babban burin Ankara shi ne kada wasu abubuwan da ba su kamata ba su jawo ɓarnar da “ba za ta gyaru ba” a tsakanin Moscow da Baku, in ji Erdogan yayin da yake magana da manema labarai a cikin jirgi a kan hanyarsa ta komawa gida da daga Azerbaijan.

RelatedPosts

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

Da yake magana kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin Armenia da Azerbaijan, Erdogan ya ce: “Za mu shaida buɗe sabbin damarmaki ta hanyar yarjejeniyar zaman lafiya.”

Game da hanyar Zangezur, wata hanya mai muhimmanci da za ta haɗa yammacin Azerbaijan da yankin Nakhchivan da kuma zama wata mahaɗa daga China zuwa Turkiyya da Rasha, Shugaba Erdogan ya ce wannan hanya tana bayar da dama ba kawai ga Azerbaijan ba, har ma ga dukkan yankin.

Ya bayyana cewa Ankara tana kallon wannan hanya a matsayin wani ɓangare na “juyin juya halin tattalin arziki.”

Ko da yake Armenia ta fara nuna adawa da hanyar Zangezur, yanzu Yerevan tana nuna sassaucin ra’ayi wajen shiga cikin haɗin kan tattalin arziki, in ji shi.

Game da batun isar da jiragen F-35 tsakanin Washington da Ankara, Shugaba Erdogan ya ce yana sa ran a fara isar da jiragen F-35 zuwa Turkiyya a hankali a lokacin mulkin Trump, yana fatan shugaban na Amurka zai “cika alkawarinmu.”

Batun F-35 ba kawai game da fasahar soja ba ne ga Turkiyya, in ji Shugaba Erdogan, yana mai cewa: “Haka ma game da karfafa hadin kai a mataki na duniya, musamman NATO.”

Ana samun rashin ɗorewar zaman lafiya a yankin saboda karya yarjejeniyar tsagaita wuta da Isra’ila ta yi, in ji Shugaba Erdogan, yana mai cewa Ankara tana aiki don hana sake faruwar hakan a wannan karon.

Turkiyya ta yi imani cewa yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Iran da Isra’ila ta kuma bude kofa ga yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, in ji shugaban, yana mai cewa Hamas ta sha nuna kyakkyawan niyya a kan wannan batu.

Game da Syria, Erdogan ya ce Türkiye ta bayyana iyakokinta a fili kan Syria, yana mai cewa kasar ba za ta yarda da kowane shiri da ke neman halatta ƙungiyoyin ta’addanci ko abokan aikinsu ba.

 

Tags: Arewa radioBBC hausafreedom radiorfi hausavoa hausa
Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Tsohon Ministan Shari’a Abubakar Malami Ya Sanar Da Ficewa Daga Jam’iyyar APC Zuwa Jam’iyyar ADC

Next Post

Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II, Ya Karɓi Gaisuwa Daga Sardaunan Kano, Malam Ibrahim Shekarau

aksam

aksam

RelatedPosts

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi  Annabi Muhammadu SWA  A Garin Nkawkawo
Uncategorized

Irin Yadda Aka Gudanar Da Zagayen Mauludn Tunawa Ga Ranar Da Aka Haifi Annabi Muhammadu SWA A Garin Nkawkawo

by aksam
September 1, 2026
Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka
Uncategorized

Kasar Ghana Ta Bayyana Shirinta Na ƙara Samar Da Wutar Lantarki Domin Sayarwa Najeriya Da Sauran ƙasashen Yammacin Afirka

by aksam
August 26, 2026
Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano
Uncategorized

Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kano Ta Dakile Wata Gobara A Rano

by aksam
August 26, 2026
Gwajin DNA: Kashi 23.6% Na Gwaje-Gwajen Uba A Najeriya Sun Nuna Rashin Daidaito
Uncategorized

Gwajin DNA: Kashi 23.6% Na Gwaje-Gwajen Uba A Najeriya Sun Nuna Rashin Daidaito

by aksam
August 25, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Naira ta cigaba da samun tagomashi a kasuwar canji

Naira ta cigaba da samun tagomashi a kasuwar canji

February 27, 2024
Babban Limamin Masallacin Juma’a  Na Tudun Biri Dake Kaduna Sheikh Imam Hashimu Jafar Ya Suke Lamirin Masu Cewa; Zasu Kai Gwamnati Kara

Babban Limamin Masallacin Juma’a Na Tudun Biri Dake Kaduna Sheikh Imam Hashimu Jafar Ya Suke Lamirin Masu Cewa; Zasu Kai Gwamnati Kara

December 15, 2023
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media