• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Akwai Yuwuwar NNPC Ya Sake Fitar Da Sabon Farashin Man Fetur A Najeriya

aksam by aksam
October 6, 2024
Reading Time: 2 mins read
0
Home LABARAI
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

Daga Hassan Umar Gwammaja

Bayan samun tataccen man fetur da ya kai lita miliyan 103 daga matatar mai ta Ɗangote a tsakankanin 15 da 30 ga watan Satumba, Kamfanin Mai na ƙasa, NNPC ya shirya tsaf domin sake fasalin farashin man kamar yadda wasu da ke da masaniya kan wannan yunƙuri suka shaida wa PREMIUM TIMES.

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

Matatar ta yi nasara bai wa motocin dakon mai 2,207 cikin 3,621 da suka je domin ɗaukar man. Motocin sun yi nasarar ɗibar lita 102,973,025 cikin lita 400,000,000 da aka tsara fitarwa daga cikin lita miliyan 25 a kullum da kamfanin ya yi alƙawarin tacewa. Wanda hakan ke nuna kaso 26% na irin ƙoƙarin da kamfanin ya yi kamar yadda PREMIUM TIMES ta gane wa idanunta.

Kamfanin NNPC ya fara dakon man ne daga matatar man Ɗangote a ranar 15 ga Satumbar 2024 a matsayin kamfanin da kaɗai zai riƙa cinikayyar mai da kamfanin kai tsaye.

A wannan rana dai, kamfanin ya fitar da sanarwa sayen mai daga daga wajen Ɗangote a kan Naira 898.78 na kowacce lita tare da sayarwa ga ‘yan kasuwa kan Naira 765.99 wanda hakan ke nuna ta sa tallafi na Naira 133 a kowacce lita da ta sayar musu.

Sai dai tun wannan lokaci ne ake cigaba da samun ƙaruwar farashin man a gidajen man NNPC ɗin a faɗin ƙasar nan, inda farashin ya kai Naira 855 zuwa Naira 897 a wasu wuraren.

Sai dai wata majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa a yanzu irin wancan man da kamfanin NNPC ya shigo da shi daga ƙetare ya ɗau ƙarewa, inda za ta fara dogara da man da za ta fara samu daga matatar Ɗangote, akwai yuwuwar kamfanin ya sake daidaita farashin da abin da ya siya daga matatar.

A halin yanzu dai ba a san yaya farashin zai kasance ba, kuma duk wani ƙoƙarin na samun babban jami’in yaɗa labarai an kamfanin NNPC, Femi Soneye, ta waya ya cutura domin bai ɗaga kiran da aka iya masa domin yin ƙarin haske kan wannan batu

Kodayake, kamfanin ya saki wani jadawali na farashi a ranar 16 ga watan Satumba, inda ya bayyana farashin yadda man zai kasance a gidajen mai a faɗin ƙasar nan bayan samun wancan mai na farko daga matatar man Dangote. Farashin, a jihar Legas, ya kama Naira 950.22 duk lita ɗaya, inda a jihar Ribas zai kama Naira 980.22 da Naira 992.22 a Abuja.

Sannan kamfanin ya nuna cewa za a sayar da shi wancan mai a kan Naira 999.22 a Arewa maso yamma, inda a Barno da sauran jihohin da ke Arewa maso Gabas za a sayar da man a kan Naira 1,019.

Har’ila yau, za a sayar da man a kan Naira 980.22 a jihohin Kudu-maso-gabas, sai kuma Naira 960.22 a kan kowacce lita a jihohin Kudu -maso-yamma (Oyo, Ogun, Ekiti, Osun, Ondo) .

Sai dai wani ɗan cikin gida a kamfanin NNPC, ya ce wannan farashi na 16 ga watan Satumba ya tashi daga aiki domin kuwa farashin kuɗin musayar kuɗi na cigaba da sauyawa, kuma ga batun tashin farashin man saboda yaƙin da ake yi a Gabas ta tsakiya.

Majiyar ta ce a yanzu farashin ya kai Dala 78 na kowacce gangar mai a yayin da ake canzar da Dalar a kan Naira 1660, don haka ba yadda za a yi farshin mai ya haura 1350 a Najeriya.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar Ya Yabawa Gwamnan Sim Fubara, Bisa Kawo Karshen Siyasar Ubangida a Jihar Rivers

Next Post

Ba Zai Yiwu A Siyar Da Litar Mai Kasa Da Naira 1,350 Ba A Najeriya:- NNPCL

aksam

aksam

RelatedPosts

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta
LABARAI

Sarkin Zurmi Ya Rasu Bayan Shekaru Biyar A Kan Sarauta

by Khadija Maitaya
September 1, 2026
Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute
LABARAI

Kano State Govt ends 50 year BUK/Rimin zakara Land Dispute

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Gwamnatin Kano Ta Jaddada Haɗin Gwiwa Tsakanin Kafafen Yaɗa Labarai da Hukumomin Tsaro
LABARAI

Yaki da harkar Daba a Jihar Kano

by Khadija Maitaya
August 31, 2026
Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo
LABARAI

Babban Malami Ya Kalubalanci Gwamnoni da ’Yan Majalisa Bisa Rufe Cibiyoyi 10 Na Yin Fasfo

by Khadija Maitaya
August 30, 2026

Recommended.

El acceso a plataformas de casino en línea es una cuestión crítica para jugadores apasionados y prof

April 21, 2025
Pakistan na daga da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran

Pakistan na daga da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Iran

April 7, 2026
ADVERTISEMENT

Trending.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

Masu Siye Da Siyar Da Filaye A  R/zakara Sunkoka Da Aibantasu Da Gwamnatin Kano Keyi.

August 26, 2026
Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

Cristiano Ronaldo Ya Auri Georgina Rodríguez

August 12, 2026
Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

Wani Kauran Mata Ya Jikkata Wata Dattijuwa Bayan Ta Hana Shi Shiga Gurin Da Bai kamata Ba

August 29, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

Kotu Ta Yanke Wa Matar Aure Hukunci Bayan Samunta Da Watsa Tafasasshen Ruwa Ga Kishiyarta

August 7, 2026
Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

Iran Ta Kakkabo Wasu Manyan Jiragen Yaƙi Na Amurka

August 14, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media