An fara babbar jarrabawar kammala sakandare, watau jarrabawar neman shiga jami’a ta kasar Sin da aka fi sani da Gaokao.
A cewar ma’aikatar ilimi ta kasar, jimillar dalibai miliyan 13.35 ne ake sa ran za su rubuta jarrabawar a bana.
Yayin rangadin da ya yi a makarantar midil ta Taiyuan dake lardin Shanxi na arewacin kasar Sin, mataimakin firaministan Sin Ding Xuexiang, ya nanata bukatar tsare adalci da tabbatar da tsaro yayin jarrabawar ta kasa.
Ding Xuexiang wanda kuma mamba ne na kwamitin dindindin na ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya kara da cewa, jarrabawar na da muhimmanci ga ayyukan raya kasa da makomar iyalai.
Ya kuma bukaci hukumomi su daukaka adalci a matsayin kashin bayan jarrabawar da na samun gurbin karatu da tsarin jarrabawar ta Gaokao. Yana mai bayyana muhimmancin tabbatar da matakan tsaro yayin jarrabawar da matakan yaki da magudin jarrabawa da ma ba dalibai goyon baya. (Fa’iza Mustapha)











