• About
  • Advertise
  • Privacy & Policy
  • Contact
AKSAM
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO
No Result
View All Result
AKSAM
No Result
View All Result

Rundunar ’Yan Sanda Sun Musanta Rahotannin Sace Kiristoci 170 A Kaduna

aksam by aksam
January 20, 2026
Reading Time: 1 min read
0
Home TSARO
ADVERTISEMENT
466
SHARES
1.5k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Daga: Hassan Umar Gwammaja

RelatedPosts

IGP Ya Umarci CPs Su Yi Bincike Kan Makamai da Harsasai

Rundunar Ƴansandan Nijeriya Ta Kama Wasu Matasa Biyu; Bisa Zarginsu Da Yin Damfara Da Sunan Su Aljannune

Rundunar ‘Yan Sanda Reshin Jihar Gombe Ta Dawo Da Dokar Hana Zirga Zirgar Babura A Jihar

Ta musanta rahotannin da ke cewa an sace wasu mabiya addinin Kirista aƙalla 163 a yankin ƙaramar hukumar Kajuru.

Jaridar Aksam Media ta ruwaito Kakakin Rundunar ASP Mansir Hassan yana ƙaryata rahotannin a yayin wata ganawa da manema labarai, bayan kammala taron da suka saba gudanarwa kan tsaro.

‎‎

ASP Mansir Hassan ya ƙalubalanci duk wanda yake iƙirarin sace mutanen da ya gabatar da hujja gami da jerin saunayen waɗanda aka sacen.

Yayin da yake nasa tsokaci kan lamarin, shugaban ƙaramar hukumar ta Kajuru, Dauda Madaki, ya ce jita-jita ce aka yaɗa amma ba wani abu ba ne face ƙanzon kurege.

 

A cewarsa, ya jagoranci tawagar jami’an tsaro zuwa Kurmin Wali, yankin da aka yi iƙirarin a nan ne aka sace mutanen sama da 160, amma sai suka iske cewar labarin na ƙarya ne.

Da yammacin ranar wannan Litinin wasu kafafen yaɗa labarai suka ruwaito labarin sace ɗimbin mutanen daga kamfanin dillancin labarai na AFP, wanda ya ce gungun ‘yan ta’adda sun yi awon gaba da aƙalla mutane 163 mabiya addinin Kirista, bayan da suka afka wa wasu Mujami’u biyu a Jihar Kaduna da ke yankin arewa maso yammacin Najeriya

Kamfanin dillancin labaran na AFP, ya ci gaba da cewa, shugaban ƙungiyar Kiristocin Najeriya reshen arewacin ƙasar, Rabaran Joseph Hayab, ya shaida masa cewar, daga labarin da suka samu ’yan ta’addan sun kai harin ne a ranar Lahadin da ta gabata, inda suka tasa ƙeyar masu bautar cikin daji.

A cewar AFP, Hayab ya ce da fari mutane 172 ’yan ta’addan suka sace, amma daga bisani 9 suka tsere.

A baya dai rahotanni sun ce adadi mai yawa na ‘yan bindigar sun farwa Majami’un biyu ne inda suka yi musu ƙawanya kafin daga bisani su sace mutanen.

Share186Tweet117SendShare
ADVERTISEMENT
Previous Post

Next Post

Rundunar Yan Sandan Nijeriya ta Gaskata sace Gomman Kiristoci a Jihar Kaduna

aksam

aksam

RelatedPosts

IGP Ya Umarci CPs Su Yi Bincike Kan Makamai da Harsasai
TSARO

IGP Ya Umarci CPs Su Yi Bincike Kan Makamai da Harsasai

by Khadija Maitaya
May 5, 2026
Rundunar Ƴansandan Nijeriya Ta Kama Wasu  Matasa Biyu;  Bisa Zarginsu Da Yin  Damfara Da Sunan Su Aljannune
TSARO

Rundunar Ƴansandan Nijeriya Ta Kama Wasu Matasa Biyu; Bisa Zarginsu Da Yin Damfara Da Sunan Su Aljannune

by aksam
April 16, 2026
Rundunar  ‘Yan Sanda  Reshin Jihar Gombe Ta Dawo Da Dokar Hana Zirga Zirgar Babura A Jihar
TSARO

Rundunar ‘Yan Sanda Reshin Jihar Gombe Ta Dawo Da Dokar Hana Zirga Zirgar Babura A Jihar

by aksam
April 2, 2026
DSS Sun Kubutar Da Sakataren Karamar Hukumar Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A Kano
TSARO

DSS Sun Kubutar Da Sakataren Karamar Hukumar Da Aka Yi Garkuwa Da Shi A Kano

by aksam
March 25, 2026

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Recommended.

Yadda Hadarin mota ya halaka fiye da mutane 42

Yadda Hadarin mota ya halaka fiye da mutane 42

March 29, 2024
Inna LillaHi Wa Inna IlaiHi Raji’un Allah Ya Jikan Haruna Dauda Biu Wakilin Muryar Amurka Na Jihohin Borno Da Yobe

Inna LillaHi Wa Inna IlaiHi Raji’un Allah Ya Jikan Haruna Dauda Biu Wakilin Muryar Amurka Na Jihohin Borno Da Yobe

May 18, 2025
ADVERTISEMENT

Trending.

Mu Na Gayyatar  ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr.  Usaini Sani Adamu !!!

Mu Na Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Gurin Daurin Auren:- Comr. Usaini Sani Adamu !!!

April 24, 2026
Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

Ga Sakon Bangajiya Daga: Angon Umar SA’ID

April 20, 2026
Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

Shekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano

May 4, 2026
Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

Muna Gayyatar ‘Yan Uwa Da Abokanan Arziki Zuwa Daurin Auren;- UMAR SA’ID

April 17, 2026
Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

Atiku, Kwankwaso , Obi Sun Jagoranci Zanga-Zanga A Babban Birnin Tarayya Abuja

April 8, 2026

Aksam Hausa

AKSAM MEDIA is a company which designed as online News Platform and other activities related to develop society.

The AKSAM MEDIA created since November 2019 and it does many activities as News publishes it publishes a Hausa News And English News.

No Result
View All Result
  • Home
    • KOTU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • KIMIYA DA FASAHA
  • LAFIYA
  • TSARO

© 2023 Aksam media