Sarkin Kano na 16, Alhaji Muhammad Sanusi II ya ce galibin matsalolin da Najeriya ke fuskanta a yanzu gadarsu aka yi.
Sarkin ya bayyana haka ne a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar gwamnatin jihar Kano da suka kai masa ziyara a fadarsa ranar Alhamis.
Sanusi ya ce bai kamata Najeriya ta ci gaba da zama wuri ɗaya ba, ya kamata ta yi huɓɓasa domin magance ƙalubalen da suka zame mata ƙarfen ƙafa.
A cewarsa, yana da ƙwarin guiwar za a iya kawo karshen dukan ƙalubalen idan aka jajirce, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito
“Ina da yaƙinin ƙalubalen da suka addabi ƙasar nan gadonsu muka yi, haka jihohi duk sun gaji matsaloli to amma ya kamata mu sani kuka ba shi ne maganin damuwar ba.
“Ba zai yiwu mu tsaya muna kokawa kan abubuwan da suka faru a baya ba tare da mun ɗauki matakin gyara ba.
“Abin da ya fi kyau shi ne ka jagoranci al’umma ta yadda za su iya tsayawa da kafafuwansu kuma kada su durkusa ma kowa.”










